Shugaban Cocin INRI Evangelical Spiritual Church, Primate Elijah Ayodele, ya bayyana cewa nasarar Shugaba Bola Tinubu na neman wa’adi na biyu a zaɓen 2027 za ta dogara ne sosai ga goyon bayan Arewa, ba wai na Yamma ko ƙungiyoyin goyon bayan Tinubu kamar City Boys Movement ba.
Ayodele ya yi wannan jawabi ne ga mambobin cocinsa, wanda aka samu a cikin bidiyo da ke yawo a kafafen sada zumunta ranar Talata, inda ya ce ƙididdigar siyasa kafin zaɓen shugaban ƙasa na gaba za ta kasance a hannun masu jefa ƙuri’a da ƙungiyoyin iko a Arewa.
- Gwamnatin Filato Ta Sassauta Dokar Hana Fita A Jos Ta Arewa
- INEC Ta Gyara Jadawalin Zaben 2027 Tare Da Tsawaita Wa’adin Mika Rajistar Jam’iyyun Siyasa
“Arewa ba ta fara goyon baya ga Tinubu ba; su ne za su yanke makomarsa,” in ji Ayodele.
Ya ƙara da cewa goyon bayan ƙabilanci daga yankin Yammacin Nijeriya ba zai isa ya tabbatar da nasara ga Shugaban ƙasa ba, duk da cewa ɗaukacin yankin na goyon bayansa. “Biliyan ɗaya na ’yan Yoruba ba za su iya yanke makomar Tinubu ba; watakila Tinubu zai yi nasara, amma Arewa ce za ta yanke hukunci, kuma hukuncin su na nufin kada ya ci.”
A cikin bidiyon, faston ya yi watsi da tasirin tallan siyasa da gangamin matasa, musamman na ƙungiyoyin goyon bayan Tinubu da ɗansa Seyi Tinubu ya kafa, wato “City Boys Movement,” yana mai cewa duk ƙoƙarin su ba zai iya tabbatar masa da nasara ba. “Babu ’yan City Boys da za su sa ka ci; Arewa ce za ta yanke makomar wa’adin Tinubu na biyu.”
Wannan jawabi na Ayodele ya zo ne a lokacin da ake ci gaba da ganin sauye-sauyen tsare-tsare a siyasa kafin zaɓen 2027, musamman ganin yadda masu adawa da dawowar Tinubu a Arewa ke ƙaruwa saboda tsaro da matsalolin rayuwa a yankin.















Discussion about this post