Askarawan Kare Al’ummar Jihar Zamfara, sun gabatar da wasu mutane tara da suka kama a Gusau, wadanda suka hada da ’yan bindiga, masu ba su bayanan sirri, masu kai musu kayayyakin aiki da kuma wani mutum da ke ikirarin cewa shi lauya ne alhali ba haka ba.An kama mutanen ne a yayin wasu samame da jami’an suka gudanar bisa bayanan sirri a sassa daban-daban na jihar.
Kwamandan Askarawan Kare Al’ummar, kuma tsohon Mataimakin Sufeto-Janar na ’Yansanda (AIG), Shehu Dalijan, ne ya bayyana hakan a lokacin da yake gabatar da wadanda ake zargin a gaban manema labarai a ranar Laraba.Daga cikin wadanda aka gabatar akwai matashi mai shekaru 20, Abubakar Malan Ori, wanda ya amsa cewa ya shafe watanni yana cikin sansanin shahararren shugaban ’yan bindiga, Kachalla Gwaska.
Ori ya ce ya shiga ayyukan ’yan bindiga a jihohin Zamfara, Kaduna da Neja, da kuma Jamhuriyar Nijar, inda ya bayyana cewa an karbi sama da Naira miliyan 226 a matsayin kudin fansa daga garkuwa da mutane daban-daban.
Haka kuma, an gabatar da Mamman Haruna da Aliyu Lawali, wadanda suka bayyana yadda suka shiga ayyukan satar shanu da hare-hare tare da wasu fitattun shugabannin ’yan bindiga.
A wani gagarumin mataki da ya raunana hanyar samun tallafin ’yan bindiga, Askarawan sun kuma kama wani likitan ’yan bindiga mai suna Ibrahim Mafindi Titus, wanda ake zargin yana kula da ’yan ta’addan da suka samu raunuka, tare da amfani da magungunan da ake samo su daga kasashen waje.
Sauran wadanda aka kama sun hada da masu ba da bayanan sirri, masu samar da kayayyakin aiki, ’yan kasuwar miyagun kwayoyi da sauransu.














