Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya kai ziyara ranar Alhamis gidan tsohon gwamnan jihar Ribas, Rotimi Amaechi, da ke Abuja bayan kammala zaɓen fidda gwani na shugaban kasa na jam’iyyar ADC.
Atiku ya samu rakiyar tsohon gwamnan jihar Sokoto, Aminu Tambuwal, tsohon shugaban jam’iyyar ADC na kasa, Ralph Nwosu, da sauran shugabannin jam’iyyar.
Ziyarar na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da furta albarkacin baki kan zaɓen fidda gwani na ADC, inda Atiku da Amaechi suka kasance manyan masu neman takarar.
LEADERSHIP ta rawaito cewa Atiku ya lashe tikitin takarar shugaban kasa na ADC bayan zaɓen fidda gwani kai tsaye da kuri’u 1,846,370, yayin da Amaechi ya samu kuri’u 504,117, sannan Mohammed Hayatu-Deen ya samu kuri’u 177,120.
An bayyana cewa ziyarar na daga cikin kokarin da ake yi na ci gaba da tuntuɓar juna domin ƙarfafa haɗin kan jam’iyyar bayan zaɓen fidda gwani mai cike da cece-kuce gabanin babban zaɓen shekarar 2027.















Discussion about this post