Shugaban hukumar kula da ayyukan kungiyar Tarayyar Afrika (AU) Mahomoud Ali Youssouf, ya ce matakin Sin na soke haraji baki daya kan kayayyakin kasashen Afrika, ya zo a daidai lokacin da ake bukata, yana cewa zai taimaka wa nahiyar tunkarar kalubalen da duniya ke fuskanta.
Mahomoud Ali Youssouf, ya bayyana haka ne yayin hira da manema labarai jiya a hedkwatar AU da ke Addis Ababa na Habasha, bayan kaddamar da taro irinsa na farko na ‘yan kasuwar Sin da Afrika.
A cewarsa, shirin na Sin yana da matukar muhimmanci, musammam a lokacin da Afrika ke fama da radadin rashin tabbas na duniya.
Daga ranar 1 ga watan Mayun bana, Sin za ta fara aiwatar da matakan soke haraji baki daya ga dukkan kayayyakin da suka fito daga kasashen Afrika 53 da ke da huldar diplomasiyya da ita. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)















Discussion about this post