Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da wani kwamitin haɗin gwuiwar ma’aikatu domin duba rawar da hukumomin tsaro da masu taimaka musu (para-military) ke takawa, ciki har da Ƴansanda, da DSS da NSCDC, a ƙoƙarin daidaita tsarin tsaron Nijeriya. Sakataren Gwamnatin Tarayya, Sanata George Akume, ne ya ƙaddamar da kwamitin a Abuja a ranar Laraba.
Akume, wanda Babban Sakataren Ofishin Aiyuka, Dr Ibrahim Abubakar Kana, ya wakilta, ya ce yawaitar hukumomin tsaro a matakan tarayya da jihohi na haifar da maimaituwar aiyuka, rikicewar hurumin aiki da kuma rashin inganci. Ya ce rahoton kwamitin zai taimaka wajen jagorantar gwamnati wajen yanke shawara kan yadda za a tsara waɗannan hukumomi yadda ya dace.
Kwamitin zai tattara bayanai kan dukkan hukumomin tsaro, su duba dokoki da aiyukansu, da tantance inda suke yin karo da juna da kuma nazarin tasirin sababbin hukumomi. Haka kuma zai duba yadda hukumomin ke aiki tare tare da gabatar da shawarwari domin ƙara inganta aiki da rage maimaituwa.
An ce kwamitin zai bayar da shawarwari kan matakan doka da tsarin aiki, ciki har da yiwuwar haɗewa, da sake fasali ko rushe wasu hukumomi idan ya zama dole.
Mambobin kwamitin sun fito daga Ƴansanda, da DSS, da sauran ma’aikatun tsaro, da harkokin ƴansanda da cikin gida, da NSCDC da ofishin mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro, kuma ana sa ran za su gabatar da cikakken rahoto cikin wa’adin da aka ƙayyade.















Discussion about this post