ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ayyukan Ta’addanci A Jihar Kano: Ina Mafita?

by Bello Hamza
5 months ago
kano

Masu nazarin harkokin yau da kullum sun bayyana cewa, ƙaruwar ayyukan ta’addanci musamman a cikin wannan watar ta Janairu 2026 a Jihar Kano ya ta’allaƙa ne saboda wasu dalilai masu dangantaka da juna. Dalilan kuma sun haɗa daga ayyukan masu aikata laifuka a cikin unguwanni da kuma yadda aka samu watsowar vurvushin bazuwar ƴan ta’adda daga wasu yankunan ƙasar nan.

A wani hari na baya-baya nan da wasu vata gari suka shiga har cikin gida suka kashe matar aure da ƴa’yan 6, abin da ya tayar da hankulan al’umma. Haka kuma ya tsananta buƙatar neman mafita tare da kawo ƙarshewn irin waɗannan kisan babu gaira babu dalili.

  • Gwamnan Kano Ya Yi Allah-wadai Da Kisan Uwa Da ‘Ya’yanta 6, Ya Umarci A Kamo Masu Laifin
  • Kisan Gillar Mutum 7 A Kano: Sarakuna Da Malamai Da Iyaye Sun Nemi A Gaggauta Yanke Wa Waɗanda Ake Zargi Hukunci

Bayanai sun nuna cewa, faɗaɗar ayyukan ƴan ta’adda daga jihohi maƙwabta kamar Zamfara da Kaduna da Katsina ya bazu zuwa wasu ƙananan hukumomin da ke maƙwabtaka da waɗannan jihohin. Idan za a iya tuna farmakin ƴan ta’adda da ake yawaitar samu a wajajen ƙarshen shekarar 2025 a wasu ƙauyukan ƙaramar hukumar Shanono. Hare haren sun haɗa da garkuwa da mutane musamman mata da yara ƙanana da sace-sacen shanu haka kuma an samu faɗace-faɗace a tsakanin jami’an tsaro da ƴan bindigan a wasu wurare.

ADVERTISEMENT

Wani vangare da masana suka tabbatar da suna bayar da gudummawa wajen haifar da ƙarin hare-hare da ayyukan ta’addanci a birarenmu sun haɗa da matsalolin zamantakewa na iyalai wanda yakan kai ga haifar da rikiice-rikice, misali shi ne irin harin da aka kai a unguwar Chiranci wanda ya yi sanadiyyar mutuwar matar aure da ƴa’yanta 6. Domin wanda ake zargin ya jagoranci kai harin ɗanuwa ne ga matar kuma suna fama rikici ne a tsakaninsu na abin da ya shafi rabon gado.

Haka kuma a ƴan shekarun nan Jihar Kano musamman ƙwaryar birnin ya fuskanci hare-hare da rikice-rikiice a tsakanin ƙungiyoyin ƴan daba na unguwanni irin wannan faɗace-faɗace ya fi ƙamari a ungunnin Kurna Mayanka da Tudun Fulani. A bayyane yake yadda waɗannan matasa suke yawo ɗauke da muggan makamai suna kai wa juna harin ramuwar gayya. Waɗannan matasan sune kuma suke a kan gaba wajen ƙwacen waya. Matane da dama sun rasa rayukansu a sanadiyyar hari da makami a yayin da ake ƙoƙarin ƙwace musu waya a unguwanni da dama a birnin Kano.

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Duk da ƙoƙarin ƙungiyoyi irin su NDLEA da HISBA da sauran jami’an tsaro, safara da shaye-shayen muggan ƙwayoyi ya ci gaba da bunƙasa a tsakanin matasa a sassan Kano. Wannan mummunan aikin ya ratsa har cikin gidaje inda ake saman matan aure da ƴan mata suna ta’ammali da muggan ƙwayoyi. Wanda mu’amala da muggan ƙwayoyin ake yi ke ƙara ayyukan masu aikakata laifukka a tsakanin al’umma a faɗin jihar.

Xaukar doka a hannu a tsakanin matasa ya ƙara haifar da matsalolin tsaro a, a watan Mayun shekarar da ta gabata a garin Rano wasu matasa sun yi sanadiyyar mutuwar wani DPO na ƴansanda sakamakon rufe shi da duka da suka sakamakon wani savani da aka samu a tsananin su. A wasu lokutta ma ana samun hare-hare inda wasu ke ɗaukar nauyin ƴan ta’adda domin su kashe musu abokan hamayyar su.

Tabbas ana fuskantar matsalolin tsaro a Jihar Kano kamar yadda yake a yawancin jihohin ƙasar nan musamman a arewacin ƙasar nan, amma yadda ake samu bazuwar ƙananan makamai abu ne mai tayar da hankali. Dole a yaba wa jami’a tsaro a kan irin wannan nasarar da suke samu domin hakan yana daƙile ayyukan masu aikata laifi. Amma wani hanzari ba gudu ba, dole a rinƙa tabbatar an hukunta dukkan waɗanda aka kama da laifi. Hakan zai ƙarfafa wa al’umma wajen bayar da bayanan sirri ga jami’an tsaro ta yadda za a ci gaba da kama masu aikata laifukka.

Haka kuma ya kamata gwammnati ta tabbatar da an samar wa jami’an tsaronmu cikakken kayan aiki, ta yadda za su gudanar da ayyukansu na kare al’umma cikin jin daɗi. A kuma bayar da muhimmanci ga albashi da kuɗaɗen sallama da kuɗaɗen da ake ba iyalan jami’an da suka rasa rayukansu a fagen fama.

An tabbatar da cewa, matsalolin tattalin arziƙi, jahilci da tsadar rayuwa suna taimakwa wajen ƙaruwar ayyukan ta’addanci. An ƙiyasta cewa, akwai kashi 33.3 na matasanmu da suke garanramba ba tare da aikin yi ba a biranen mu wanda hakan yake ƙara zafafa ayyukan ta’addanci a tsakanin matasan.

Ya kuma kamata ƴan siyasa su gudanar da ayyukan ci gaban al’umma kamar yadda suka yi alkawari a lokuttan da suke yaƙin neman zave. Su kuma matasa ya kamata su yi wa kansu karatun ta natsu wajen ƙin yarda a yi amfani da su wajen kai hare-hare ga abokan hamayyar siyasa, musamman yanzu da aka shiga lokuttan harkokin siyasa.

ina mai yaba wa da ƙoƙarin rundunar ƴansanda Jihar Kano a kan yadda ta yi amfani da ƙwarewar ta wajen zaƙulo cikin gaggawa waɗanda suka yi kisan na Xorayi Charancci. Tabbass sun nuna ƙwarewa da kishin ƙasa da fatan hakan zai ɗore. Allah ya ci gaba da kawo mana zaman lafiya a unguwanninmu jihohinmu da ƙasar mu gaba ɗaya.

kano
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata

MASU ALAKA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya
Labarai

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Next Post
Adadin Ikon Mallakar Fasaha A Kasar Sin Ya Kai Miliyan 5.32

Adadin Ikon Mallakar Fasaha A Kasar Sin Ya Kai Miliyan 5.32

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.