ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Ni Da Alaƙa Ko Hannu A Ta’addanci – Gwamnan Bauchi

by Sadiq Usman
6 months ago

Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Abdulkadir Mohammed, ya bayyana cewa ba ɗan ta’adda ba ne kuma ba shi da wata alaƙa da ta’addanci ko wani laifi.

Gwamnan ya faɗi hakan ne a ranar Laraba a Fadar Gwamnati da ke Bauchi, yayin da yake karɓar lambar yabo ta Award of Excellence a matsayin Jakadan Tsaro daga Cibiyar Tsaro ta Nijeriya (Safety Institute of Nigeria).

  • Jam’iyyar NNPP Ta Yi Watsi Da Dakatarwar Da Aka Yi Wa Dungurawa A Kano
  • Dubu 100 Aka Biya Ni Na Sanya Bam A Masallaci A Borno — Ɗan Ƙunar Baƙin Wake

Ya yi wannan jawabi ne domin mayar da martani ga rahotannin da ke danganta shi da ta’addanci, da kuma ci gaba da tsare Kwamishinan Kuɗi na jihar da Hukumar EFCC ke yi.

ADVERTISEMENT

Yayin karɓar lambar yabon, Mohammed ya ce, “Na kasance jakadan tsaro. Ban san cewa abu ne mai girma haka ba sai da wannan mai gabatarwa ya yi bayani sosai. Ina matuƙar farin ciki da karɓar wannan lambar yabo a madadin mutanen Jihar Bauchi.”

Ya ƙara da cewa wannan girmamawa ba tasa ce shi kaɗai ba, illa ta mutanen Jihar Bauchi gaba ɗaya.

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Fitaccen Kwamandan ’Yan Bindiga, Kachalla Sani Yellow A Zamfara

2027: INEC Ta Tsawaita Wa’adin Miƙa Sunayen ’Yan Takara

Gwamnan ya bayyana mamakinsa kan zarge-zargen da ake yi masa, inda ya ce, “Ina farkawa kawai na ga ana zargina da ta’addanci a matsayina na Gwamna.”

Ya kuma koka kan abin da ya kira rashin adalci daga hukumomin tarayya.

A cewarsa, “Ko da yake ina da kariya ta doka a matsayina na Gwamna, an ambaci sunana a wata kotu ta Nijeriya.”

Mohammed ya ce ya daɗe yana yin shiru ne domin tabbatar da zaman lafiya, amma yanzu ba zai ƙara yin shiru ba.

“Na yi shiru na tsawon lokaci. Na yi hakan ne saboda zaman lafiya da tsaro, amma ba matsoraci ba ne,” in ji shi.

Da yake magana kan tsaro da shugabanci, gwamnan ya ce Jihar Bauchi na ci gaba da kasancewa cikin kwanciyar hankali duk da matsalolin tsaro da ke addabar Arewacin ƙasar.

Ya ce, “Babu wata jiha a Arewa da ta fi Bauchi samun tsaro.”

Gwamnan ya zargi gwamnatin tarayya ƙarƙashin APC da amfani da hukumomin gwamnati wajen gallaza wa ‘yan adawa.

A cewarsa, “Gwamnatin tarayya ƙarƙashin APC na tunanin za ta iya amfani da kotuna da hukumomin gwamnati kamar EFCC domin muzguna wa ‘yan Nijeriya da ba sa cikin jam’iyyarsu.”

Ya yi gargaɗin cewa ba zai ci gaba da yin shiru ba.

“Ina tabbatar muku, ba za mu ƙara yin shiru ba. Ba zan yadda wani ya mayar da ni mai laifi saboda ban shiga APC ba, kuma ba zan shiga APC ba,” in ji Mohammed.

MASU ALAKA

An Kashe Fitaccen Kwamandan ’Yan Bindiga, Kachalla Sani Yellow A Zamfara
Manyan Labarai

An Kashe Fitaccen Kwamandan ’Yan Bindiga, Kachalla Sani Yellow A Zamfara

July 12, 2026
inec
Manyan Labarai

2027: INEC Ta Tsawaita Wa’adin Miƙa Sunayen ’Yan Takara

July 12, 2026
Mutum 1 Ya Mutu, 7 Sun Jikkata Yayin Da Ginin Majalisar Dokokin Gombe Ya Rufta
Manyan Labarai

Mutum 1 Ya Mutu, 7 Sun Jikkata Yayin Da Ginin Majalisar Dokokin Gombe Ya Rufta

July 11, 2026
Next Post
Sanatan Nasarawa Ta Arewa, Godiya Akwashiki, Ya Rasu Yana Da Shekaru 52

Sanatan Nasarawa Ta Arewa, Godiya Akwashiki, Ya Rasu Yana Da Shekaru 52

LABARAI MASU NASABA

Hukumomin Kasar Sin Sun Tsara Shirin Kandagarkin Ambaliyar Ruwa

Hukumomin Kasar Sin Sun Tsara Shirin Kandagarkin Ambaliyar Ruwa

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Fim ɗin ƙaddara: Anya Ana Samun Irin Wannan ƙaddarar Kuwa?

July 12, 2026
Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula

Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula

July 12, 2026
‘Lokaci Ya Yi Na Ɗaukar Mataki Kan Masu Yanke Hukunci Da Kansu’

Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

July 12, 2026
An Kashe Fitaccen Kwamandan ’Yan Bindiga, Kachalla Sani Yellow A Zamfara

An Kashe Fitaccen Kwamandan ’Yan Bindiga, Kachalla Sani Yellow A Zamfara

July 12, 2026
NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli

NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli

July 12, 2026
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

July 12, 2026
NDLEA Ta Gargaɗi Masu Sana’ar Keke NAPEP Kan Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi

NDLEA Ta Gargaɗi Masu Sana’ar Keke NAPEP Kan Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi

July 12, 2026
inec

2027: INEC Ta Tsawaita Wa’adin Miƙa Sunayen ’Yan Takara

July 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.