ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Ni Da Alaƙa Ko Hannu A Ta’addanci – Gwamnan Bauchi

by Sadiq Usman
8 months ago

Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Abdulkadir Mohammed, ya bayyana cewa ba ɗan ta’adda ba ne kuma ba shi da wata alaƙa da ta’addanci ko wani laifi.

Gwamnan ya faɗi hakan ne a ranar Laraba a Fadar Gwamnati da ke Bauchi, yayin da yake karɓar lambar yabo ta Award of Excellence a matsayin Jakadan Tsaro daga Cibiyar Tsaro ta Nijeriya (Safety Institute of Nigeria).

  • Jam’iyyar NNPP Ta Yi Watsi Da Dakatarwar Da Aka Yi Wa Dungurawa A Kano
  • Dubu 100 Aka Biya Ni Na Sanya Bam A Masallaci A Borno — Ɗan Ƙunar Baƙin Wake

Ya yi wannan jawabi ne domin mayar da martani ga rahotannin da ke danganta shi da ta’addanci, da kuma ci gaba da tsare Kwamishinan Kuɗi na jihar da Hukumar EFCC ke yi.

ADVERTISEMENT

Yayin karɓar lambar yabon, Mohammed ya ce, “Na kasance jakadan tsaro. Ban san cewa abu ne mai girma haka ba sai da wannan mai gabatarwa ya yi bayani sosai. Ina matuƙar farin ciki da karɓar wannan lambar yabo a madadin mutanen Jihar Bauchi.”

Ya ƙara da cewa wannan girmamawa ba tasa ce shi kaɗai ba, illa ta mutanen Jihar Bauchi gaba ɗaya.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

Gwamnan ya bayyana mamakinsa kan zarge-zargen da ake yi masa, inda ya ce, “Ina farkawa kawai na ga ana zargina da ta’addanci a matsayina na Gwamna.”

Ya kuma koka kan abin da ya kira rashin adalci daga hukumomin tarayya.

A cewarsa, “Ko da yake ina da kariya ta doka a matsayina na Gwamna, an ambaci sunana a wata kotu ta Nijeriya.”

Mohammed ya ce ya daɗe yana yin shiru ne domin tabbatar da zaman lafiya, amma yanzu ba zai ƙara yin shiru ba.

“Na yi shiru na tsawon lokaci. Na yi hakan ne saboda zaman lafiya da tsaro, amma ba matsoraci ba ne,” in ji shi.

Da yake magana kan tsaro da shugabanci, gwamnan ya ce Jihar Bauchi na ci gaba da kasancewa cikin kwanciyar hankali duk da matsalolin tsaro da ke addabar Arewacin ƙasar.

Ya ce, “Babu wata jiha a Arewa da ta fi Bauchi samun tsaro.”

Gwamnan ya zargi gwamnatin tarayya ƙarƙashin APC da amfani da hukumomin gwamnati wajen gallaza wa ‘yan adawa.

A cewarsa, “Gwamnatin tarayya ƙarƙashin APC na tunanin za ta iya amfani da kotuna da hukumomin gwamnati kamar EFCC domin muzguna wa ‘yan Nijeriya da ba sa cikin jam’iyyarsu.”

Ya yi gargaɗin cewa ba zai ci gaba da yin shiru ba.

“Ina tabbatar muku, ba za mu ƙara yin shiru ba. Ba zan yadda wani ya mayar da ni mai laifi saboda ban shiga APC ba, kuma ba zan shiga APC ba,” in ji Mohammed.

MASU ALAKA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
Manyan Labarai

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Next Post
Sanatan Nasarawa Ta Arewa, Godiya Akwashiki, Ya Rasu Yana Da Shekaru 52

Sanatan Nasarawa Ta Arewa, Godiya Akwashiki, Ya Rasu Yana Da Shekaru 52

LABARAI MASU NASABA

Yaya Toure Na Dab Da Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai

Yaya Toure Na Dab Da Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai

September 9, 2026
Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa

Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa

September 9, 2026
’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.