ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

by Shehu Yahaya
6 hours ago
Kaduna

Ayyukan ginawa da inganta hanyoyi da Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ke aiwatarwa sun fara haifar da sauyi mai ɗorewa a rayuwar al’ummar Ƙaramar Hukumar Sabon Gari da Zariya. 

Hanyar Dogon Bauchi zuwa Kakeyi, wacce ke da tsawon kilomita 17 tare da sabuwar gadar Kakeyi, ta zama wata babbar hanyar ci gaba da ta sauƙaƙa zirga-zirga, ta ƙara yawan yara masu shiga makaranta, ta rage asarar amfanin gona bayan girbi, tare da bunƙasa kasuwanci da tattalin arzikin yankin.

Hanyar ta taso ne daga bakin Masallacin Juma’a da ke Dogon Bauchi a Ƙaramar Hukumar Sabon Gari zuwa Kakeyi da ke Ƙaramar Hukumar Zariya.  Hanyar za ta amfani al’ummomi sama da dubu ɗari biyar, musamman manoma, ƴan kasuwa da ɗalibai da suka shafe shekaru suna fama da matsalar rashin ingantacciyar hanya.

ADVERTISEMENT

Wannan ya fito fili ne yayin wata ziyarar tantance ayyukan raya ƙasa da tawagar ƴan jarida ƙarƙashin jagorancin Kwamishinan Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Al’adu na Jihar Kaduna, Malam Ahmed Maiyaki, ta kai domin duba ayyukan da gwamnatin jihar ke aiwatarwa a sassa daban-daban.

A zantawar manema labarai, Mazauna yankunan Dogon Bauchi da Kakeyi sun bayyana cewa gina gadar Kakeyi da shimfiɗa kwalta ya kawo ƙarshen wahalhalun da suka jima suna fuskanta, musamman wajen zirga-zirga tsakanin ƙananan hukumomin Sabon Gari, Zariya da Soba.

LABARAI MASU NASABA

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

mazaunin garin Jaba, Shamsudeen Abdullahi ya ce sama da shekaru 30 manoma suna asarar amfanin gonarsu saboda rashin hanya mai kyau.

“Wannan gada da titin za su rage asarar kayan gona, su ƙara yawan masu zuwa kasuwanni, kuma sun haɗa dubban al’umma da suka dogara da noma da kasuwanci domin gudanar da rayuwarsu,” in ji shi.

Shi ma wani manomi, Ibrahim Abubakar, ya bayyana yadda rayuwarsu ta sauya bayan kammala aikin.

“Yanzu haka daga gona nake dawowa cikin motata. A da sai mun hau kwalekwale kafin mu isa gida. Allah kaɗai ya san adadin mutanen da suka rasa rayukansu sakamakon ambaliya da rashin gada.”

A ɓangaren ilimi kuwa, ɗaliban yankin sun ce sabon titin ya kawo ƙarshen wahalar da suke sha wajen zuwa makaranta. Sun bayyana cewa a baya dole ne su riƙa amfani da kwalekwale domin tsallakawa tsakanin Kakeyi da Dogon Bauchi, lamarin da ke janyo jinkiri da haɗarin rayuwa. Amma yanzu suna iya tafiya a ƙafa cikin ƴan mintuna kaɗan su isa makaranta cikin kwanciyar hankali.

Mazauna yankunan sun ce wannan sauyi ya ƙara yawan yaran da ke halartar makaranta, tare da rage yawan waɗanda ke daina karatu saboda matsalolin sufuri.

Sun gode wa Gwamna Uba Sani bisa aiwatar da ayyukan ci gaba da ya kawo musu wanda suka daɗe suna nema. Sun yi alƙawarin cewa suna jiran ranar da za su saka masa da biki. 

Da yake amsa tambayoyin manema labarai, Kwamishinan Yaɗa Labarai da Al’adu na Jihar Kaduna, Malam Ahmed Maiyaki, ya ce gwamnatin Sanata Uba Sani ta himmatu wajen samar da ingantattun hanyoyi domin bunƙasa tattalin arziki da inganta rayuwar jama’a.

Ya bayyana cewa gwamnatin jihar ta gina hanyoyi sama da 150 a faɗin Kaduna, yana mai cewa titin Dogon Bauchi zuwa Kakeyi na daga cikin ayyukan da za su rage mace-macen mata masu juna biyu da marasa lafiya da ke faruwa sakamakon rashin hanyar zuwa cibiyoyin lafiya.

A cewarsa, aikin ba wai hanya kaɗai aka gina ba, an samar da wata gada ta ci gaba wacce za ta haɗa al’umma, ta bunƙasa ilimi, noma, kasuwanci da harkokin lafiya, tare da tabbatar da cewa al’ummomin karkara sun more romon dimokuraɗiyya kamar sauran sassan jihar.

Kaduna
Shehu Yahaya
+ postsBio
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Sabbin Matakan Dakile Haɗura A Titin Bypass
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Matasa 1,200 Sun Amfana Da Horon Sana’o’i Ƙarƙashin Shirin ‘Renewed Hope’ A Kaduna
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

MASU ALAKA

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi
Labarai

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan
Labarai

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026
Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC
Manyan Labarai

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

July 4, 2026
Next Post
Gwamnan Katsina Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Cibiyar Gyaran Motoci Mai Amfani Da Hasken Rana

Gwamnan Katsina Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Cibiyar Gyaran Motoci Mai Amfani Da Hasken Rana

LABARAI MASU NASABA

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026
Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC

July 4, 2026
Gwamnan Katsina Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Cibiyar Gyaran Motoci Mai Amfani Da Hasken Rana

Gwamnan Katsina Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Cibiyar Gyaran Motoci Mai Amfani Da Hasken Rana

July 4, 2026
Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

NPA Ta Ɗaura Ɗamarar Magance Matsalolin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

July 4, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Yadda Jihohi Suka Fara Ɗanɗana Ambaliyar Ruwa A Daminar Bana

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.