ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

by Shehu Yahaya
3 weeks ago
Kaduna

Ayyukan ginawa da inganta hanyoyi da Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ke aiwatarwa sun fara haifar da sauyi mai ɗorewa a rayuwar al’ummar Ƙaramar Hukumar Sabon Gari da Zariya. 

Hanyar Dogon Bauchi zuwa Kakeyi, wacce ke da tsawon kilomita 17 tare da sabuwar gadar Kakeyi, ta zama wata babbar hanyar ci gaba da ta sauƙaƙa zirga-zirga, ta ƙara yawan yara masu shiga makaranta, ta rage asarar amfanin gona bayan girbi, tare da bunƙasa kasuwanci da tattalin arzikin yankin.

Hanyar ta taso ne daga bakin Masallacin Juma’a da ke Dogon Bauchi a Ƙaramar Hukumar Sabon Gari zuwa Kakeyi da ke Ƙaramar Hukumar Zariya.  Hanyar za ta amfani al’ummomi sama da dubu ɗari biyar, musamman manoma, ƴan kasuwa da ɗalibai da suka shafe shekaru suna fama da matsalar rashin ingantacciyar hanya.

ADVERTISEMENT

Wannan ya fito fili ne yayin wata ziyarar tantance ayyukan raya ƙasa da tawagar ƴan jarida ƙarƙashin jagorancin Kwamishinan Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Al’adu na Jihar Kaduna, Malam Ahmed Maiyaki, ta kai domin duba ayyukan da gwamnatin jihar ke aiwatarwa a sassa daban-daban.

A zantawar manema labarai, Mazauna yankunan Dogon Bauchi da Kakeyi sun bayyana cewa gina gadar Kakeyi da shimfiɗa kwalta ya kawo ƙarshen wahalhalun da suka jima suna fuskanta, musamman wajen zirga-zirga tsakanin ƙananan hukumomin Sabon Gari, Zariya da Soba.

LABARAI MASU NASABA

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

mazaunin garin Jaba, Shamsudeen Abdullahi ya ce sama da shekaru 30 manoma suna asarar amfanin gonarsu saboda rashin hanya mai kyau.

“Wannan gada da titin za su rage asarar kayan gona, su ƙara yawan masu zuwa kasuwanni, kuma sun haɗa dubban al’umma da suka dogara da noma da kasuwanci domin gudanar da rayuwarsu,” in ji shi.

Shi ma wani manomi, Ibrahim Abubakar, ya bayyana yadda rayuwarsu ta sauya bayan kammala aikin.

“Yanzu haka daga gona nake dawowa cikin motata. A da sai mun hau kwalekwale kafin mu isa gida. Allah kaɗai ya san adadin mutanen da suka rasa rayukansu sakamakon ambaliya da rashin gada.”

A ɓangaren ilimi kuwa, ɗaliban yankin sun ce sabon titin ya kawo ƙarshen wahalar da suke sha wajen zuwa makaranta. Sun bayyana cewa a baya dole ne su riƙa amfani da kwalekwale domin tsallakawa tsakanin Kakeyi da Dogon Bauchi, lamarin da ke janyo jinkiri da haɗarin rayuwa. Amma yanzu suna iya tafiya a ƙafa cikin ƴan mintuna kaɗan su isa makaranta cikin kwanciyar hankali.

Mazauna yankunan sun ce wannan sauyi ya ƙara yawan yaran da ke halartar makaranta, tare da rage yawan waɗanda ke daina karatu saboda matsalolin sufuri.

Sun gode wa Gwamna Uba Sani bisa aiwatar da ayyukan ci gaba da ya kawo musu wanda suka daɗe suna nema. Sun yi alƙawarin cewa suna jiran ranar da za su saka masa da biki. 

Da yake amsa tambayoyin manema labarai, Kwamishinan Yaɗa Labarai da Al’adu na Jihar Kaduna, Malam Ahmed Maiyaki, ya ce gwamnatin Sanata Uba Sani ta himmatu wajen samar da ingantattun hanyoyi domin bunƙasa tattalin arziki da inganta rayuwar jama’a.

Ya bayyana cewa gwamnatin jihar ta gina hanyoyi sama da 150 a faɗin Kaduna, yana mai cewa titin Dogon Bauchi zuwa Kakeyi na daga cikin ayyukan da za su rage mace-macen mata masu juna biyu da marasa lafiya da ke faruwa sakamakon rashin hanyar zuwa cibiyoyin lafiya.

A cewarsa, aikin ba wai hanya kaɗai aka gina ba, an samar da wata gada ta ci gaba wacce za ta haɗa al’umma, ta bunƙasa ilimi, noma, kasuwanci da harkokin lafiya, tare da tabbatar da cewa al’ummomin karkara sun more romon dimokuraɗiyya kamar sauran sassan jihar.

Kaduna
Shehu Yahaya
+ postsBio
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Jam’iyyar NDC Ta Shirya Tsaf Domin Kafa Gwamnati A 2027 —Kwankwaso
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Majalisar Zartarwa Ta Jihar Kaduna Ta Amince Da Manufofin Haɓaka Walwalar Al’ummar Jihar
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

MASU ALAKA

Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa
Labarai

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

July 24, 2026
Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya
Ra'ayi Riga

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

July 24, 2026
Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari
Labarai

Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

July 24, 2026
Next Post
Gwamnan Katsina Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Cibiyar Gyaran Motoci Mai Amfani Da Hasken Rana

Gwamnan Katsina Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Cibiyar Gyaran Motoci Mai Amfani Da Hasken Rana

LABARAI MASU NASABA

Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

July 24, 2026
An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

July 24, 2026
NNPP Za Ta Kwace Mulki A Jihar Imo – Kwankwaso

Jam’iyyar NDC Ta Shirya Tsaf Domin Kafa Gwamnati A 2027 —Kwankwaso

July 24, 2026
Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

July 24, 2026
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

July 24, 2026
Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

July 24, 2026
Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

July 24, 2026
Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

July 24, 2026
NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci

NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci

July 24, 2026
Sin Tana Son More Damammakin Fasahar AI a Maimakon Babakere a Wannan Bangare Da Kasashen Yamma Suka Dade Suna Yi

Sin Tana Son More Damammakin Fasahar AI a Maimakon Babakere a Wannan Bangare Da Kasashen Yamma Suka Dade Suna Yi

July 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.