ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babakeren Amurka: Munafunci Dodo Ya Kan Ci Mai Shi

by Sulaiman
5 months ago
Amurka

A ranar Talata, shafin yanar gizo na Africa Check ya watsa wani bayani, inda ya ce, wani labarin dake yaduwa a shafukan sada zumunta, cewa “Sojojin Amurka sun kai hari kan fadar shugabancin kasar Najeriya”, karya ne.

To, duk da cewa wannan labari karya ne, yaduwarsa ta nuna damuwar da mutane suke da ita a zuci. Da ma harin da aka kai kasar Venezuela a farkon watan da muke ciki ya riga ya nuna yadda kasar Amurka take wuce gona da iri, yayin da take cin zarafin sauran kasashe. Sai dai daga bisani kasar ta sake yin barazanar kai hare-hare ga dimbin kasashe dake nahiyoyin Asiya da Turai da Latin Amurka. Har ma shugaban kasar Donald Trump ya ce dokokin kasa da kasa ba su da tasiri a kansa. Wadannan abubuwa tabbas za su jefa mutanen duniya cikin damuwa, saboda sun san cewa tun da “yau an kai hari ga kasar Venezuela, to gobe ma za a iya tasam ma wata kasa ta daban.”

Hakika barazanar da kasar Amurka ta yi abu ne mai ban tsoro. Amma tsoron ya kan ragu, idan an yi tunanin yanayin da kasar ke ciki. Sanin kowa ne, a yawancin lokuta, idan aka dubi wata dabba da ke matukar haushi, da kokarin cizon mutane, za a ga dabba ce da ta fada cikin tarko.

ADVERTISEMENT

Idan mun waiwayi matakan soja da kasar Amurka ta dauka a wadannan watanni, misali yadda kasar ta kai hari kan na’urorin tace sinadaran Uranium na kasar Iran, da kutsa kai cikin kasar Venezuela, da yadda ta kai hari daga sama a kasar Najeriya, bayan da ta tilasta wa gwamnatin Najeriya yarda da hakan, to, za mu ga kusan duk matakai ne na gajeren lokaci. Niyyar kasar Amurka ita ce, a magance wani babban yaki da ya dade, sannan a yi kokarin samar da tasiri a duniya, don nuna ma mutanen duniya cewa “Har yanzu kasar Amurka tana da karfin yin babakere”. Amma ainihin yanayin da kasar ke ciki shi ne, tana fuskantar matsaloli a fannonin sabunta jiragen yaki na ruwa da na sama, da yunkurinta na farfado da masana’antu. Kana kasar ta fara rasa fifiko a dimbin fannonin kimiyya da fasaha. Yayin da sakamakon yakin ciniki da na fasaha da aka yi a shekarar 2025 ya nuna cewa, kasar Amurka ta riga ta rasa karfin kiyaye wani matsayi na babakere a duniya.

Dalilin da ya sa kasar Amurka ke son ci gaba da aiwatar da mulkin danniya, shi ne domin wani tsohon tunanin al’ummar yammacin duniya, wato yarda da manufar kashin dankali, da kuma “Bar mai cin nasara a wata takara ya mallaki kome”. A ganin masu nazarin huldar kasa da kasa na kasashen yamma, ba za a iya samun kwanciyar hankali a duniya ba, idan babu wata kasa da ta rike matsayi na babakere, wadda take ba da umarni domin sauran kasashe su bi.

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

Sai dai a wannan zamanin da muke ciki na samun bunkasar tattalin arzikin dimbin kasashe masu tasowa cikin matukar sauri, yawancin kasashe sun riga sun yi watsi da wannan tunani maras gaskiya na kasashen yamma. Wani misalin da zai iya zama shaidar hakan, shi ne, bayan da kasar Sin ta gabatar da shawarar inganta jagorancin duniya a watan Saumban bara, wadda ta jaddada muhimmancin daidaiton ikon mulkin kai na mabambantan kasashe, da kula da al’amuran duniya bisa doka, da yarda da kasancewar dimbin bangarori masu fada-a-ji a duniya, da mai da moriyar al’umma a gaban kome, da manufar daukar hakikanan matakai, zuwa yanzu shawarar ta riga ta samu goyon baya daga kasashe fiye da 150. Ban da haka, kasar Sin ita ma ta gabatar da ra’ayinta, wanda shi ma ya kasance na galibin kasashe, wajen tarukan kasa da kasa daban daban, inda ta ce: Ya kamata a daidaita huldar kasa da kasa bisa ka’idoji, maimakon barin wasu kasashe su ci gaba da yin kashin dankali. A zamanin da muke ciki, mulkin danniya ba zai samu nasara ba. Kana ya kamata manyan kasashe su zama wadanda suka fara bin doka da ka’ida.

Hakika, abin da mai aiwatar da mulkin danniya bai fahimta ba shi ne, ta karfin tuwo za a iya kwatar albarkatu da dukiya, amma ba za a iya samun amincewar jama’a ba. Kana matakin tsoratar da saura ba zai taba haifar da kauna da sahihanci ba. Yanzu mun ga yadda wata kasa ta kama hanyar faduwa, amma tana ci gaba da cin zarafin sauran kasashe, da kwace albarkatu yadda ta ga dama, amma sanin kowa ne, “munafunci dodo ne ya kan ci mai shi”. (Bello Wang)

Amurka
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Next Post
Gobara Ta Ƙone Wani Sashi Na Maƙabarta A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashi Na Maƙabarta A Kano

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.