ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

by Sulaiman
48 minutes ago
Sin

A farkon rabin shekarar bana, sakamakon yakin da ya barke tsakanin Amurka da Isra’ila da Iran, farashin mai na duniya ya yi tashin gwauron zabi, kuma matsalar makamashi ta shafi kasashe da dama, ciki har da dimbin kasashen Afirka. A ranar 31 ga Maris, gwamnatin Zambiya ta sanar da kafa dokar ta baci sakamakon matsalar samar da man fetur a kasar. Masanin ilimin makamashi na kasar, Johnstone Chikwanda, ya ce: “Muna fuskantar babbar barazana ta fannin tsaron makamashi, wadda ba Zambia kadai ta shafa ba, har da kimanin kashi 75% na sauran kasashen Afirka.”

Matsalar makamashi ta kan haifar da mummunan tasiri ga bunkasar tattalin arzikin duniya, musamman idan mun yi la’akari da matsalolin makamashi sau uku da aka fuskanta a karni na 20. Abin lura shi ne, a wannan karo, wasu kafofin yada labarai irin su Wall Street Journal na Amurka da Le Figaro na Faransa sun bayyana ra’ayin cewa: a lokacin yakin Amurka da Isra’ila da Iran, kasar Sin ba ta fafata da sauran kasashen duniya wajen sayen mai ba, kuma hakan ya taimaka wajen daidaita farashin mai a duniya, tare da ceton tattalin arzikin duniya a karo na biyu. (Karo na farko shi ne bayan rikicin kudi na duniya a shekara ta 2008, lokacin da kasar Sin ta yalwata yawan bukatun cikin gida, ta tallafa wa bukatun duniya gaba daya, wanda hakan ya taimaka wa tattalin arzikin duniya fita daga kangin koma baya.)

Me ya sa jaridun suka fadi haka?

ADVERTISEMENT

Lallai, tun bayan barkewar yakin Amurka da Isra’ila da Iran, mashigar tekun Hormuz, wacce take tamkar “makogwaron” jigilar makamashi a duniya, ta gamu da cikas sosai. A kowace rana, ana jigilar mai kusan ganga miliyan 20 ta mashigin Hormuz, wanda ya kai kashi 1/5 na man da ake jigilar a duniya. Idan mashigar ta gamu da cikas, damuwa da fargaba zai sa kasa da kasa su yi kokarin sayen mai daga kasuwannin duniya, wanda hakan zai haifar da hauhawar farashin mai. Duk da haka, kasar Sin, wacce take kan gaba wajen shigo da mai a duniya, ba ta shiga cikin kasashen da ke takarar sayen mai ba, a maimakon haka ta rage sayen mai na dan gajeren lokaci. A watan Mayu, man da kasar ta shigo da shi ya ragu zuwa ganga 780,000 a kowace rana, wanda ya ragu da kashi 29% idan aka kwatanta da makamancin lokacin a shekarar da ta gabata, kuma shi ne mai mafi karanci da ta shigo da shi tun bayan shekara ta 2018. Rage sayen mai da ya kai sama da ganga miliyan uku a kowace rana, ya sassauta damuwar kasashen da ke kokarin sayen mai a kasuwannin duniya, wanda hakan ya taimaka wajen saukar da farashin mai. Ga Afirka, wannan yana nufin an sassauta matsalar hauhawar farashin kayayyaki da ake shigarwa daga waje. Wannan shi ne dalilin da ya sa jaridun kasashe daban daban suka dauki kasar Sin a matsayin muhimmin karfi mai tallafawa kokarin daidaita rikicin mai a duniya.

Amma me ya sa kasar Sin ta iya rage sayen mai a maimakon kara sayowa a yayin rikicin? To, dalili shi ne canji mai zurfi da ta samu a tsarin makamashinta. A baya, kasar Sin ta kasance tamkar “injin” da ke kara yawan bukatun mai a duniya. Bisa ga Littafin Kididdigar Makamashi ta Duniya, daga shekara ta 2005 zuwa 2024, yawan man da kasar Sin ta yi amfani da shi ya ninka fiye da sau biyu, wanda ya kai sama da rabin yawan karuwar bukatun mai na duniya a wadannan shekaru. Amma a shekara ta 2024, an samu sauyi, inda yawan man da kasar ta yi amfani da shi a fannin sufuri ya ragu, kuma a wannan shekarar, sakamakon karuwar motocin lantarki da ake amfani da su a kasar, yawan man da ake amfani da shi a kowace rana ya ragu da ganga 430,000. Wannan canji bai faru ba zato ba tsammani ba. Tun bayan da kasar Sin ta zama kasar da yawan man da take shigo da shi ya zarce wanda take fitarwa zuwa ketare, kuma ta dogara ga kasashen ketare wajen shigo da kaso 70% na mai da take bukata, a sannan kasar ta san cewa, bai kamata a damka makomar makamashi a hannun wasu ba. A watan Mayu na shekara ta 2014, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya kai ziyara wani kamfanin kera motoci, inda ya ce: “Raya motoci masu amfani da sabbin makamashi ita ce hanya tilo da kasar Sin za ta bi don sauyawa daga kasa mai yawan motoci zuwa kasa mai karfin hada da amfani da motoci.” Bayan shekaru goma sha biyu, yawan motoci masu amfani da sabbin makamashi da aka samar a kasar ya karu daga 78,500 a shekara zuwa sama da miliyan 16, wanda ya ninka har sau 200. Ya zuwa karshen watan Mayu na shekara ta 2026, karfin samar da wutar lantarki na kasar Sin ya kai kilowatt biliyan 4.01, kuma karfinta na samar da lantarki bisa makamashin zamani ya kai kashi 62%. Kasar Sin ta gina tsarin samar da makamashin da ake sabuntawa mafi girma kuma mafi saurin bunkasa a duniya, wannan kuma ya baiwa kasar Sin karfin tinkarar rikicin.

LABARAI MASU NASABA

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

Wannan ya kuma ba wa Afirka muhimmin darasi. Afirka ita ce nahiya mafi arzikin albarkatun hasken rana, iska da ruwa a duniya, amma har yanzu akwai kusan mutane miliyan 600 da suke fuskantar matsalar rashin wutar lantarki. A shekarun baya-bayan nan, kamfanonin Sin a kasashen Najeriya, Afirka ta Kudu, Kenya, Habasha da sauran kasashen Afirka sun gina ayyukan samar da wutar lantarki ta ruwa, hasken rana da iska, wadanda ke taimakawa wajen rage dogaro ga samar da wutar lantarki daga man dizal, kuma yana baiwa kasashen Afirka damar shiga zamanin makamashi mai tsafta cikin farashi mai rahusa.

Tsaron makamashi yana shafar rayuwar iyalai da injunan masana’antu da kuma makomar kasashe. Kasar Sin bisa yadda ta gyara tsarin makamashinta, ta ba da amsarta, wato ya zama dole a tabbatar da ci gaban kasa bisa makamashin da ake sabuntawa, kuma Sin da Afirka suna iya hadin gwiwa a fannin, tare da cin gajiyarsa.

Sin
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda Takwas A Katsina
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI
  • Sulaiman
    Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

MASU ALAKA

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka
Ra'ayi Riga

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

July 7, 2026
Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC
Ra'ayi Riga

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

July 6, 2026
Ga “Itacen Kuka” Na Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ga “Itacen Kuka” Na Kasar Sin

July 1, 2026
Next Post
Ta’addanci

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda Takwas A Katsina

LABARAI MASU NASABA

Ta’addanci

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda Takwas A Katsina

July 9, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

July 9, 2026
Auto Draft

TCN Ta Kammala Gyaran Layin Wutar Lantarkin Zaria–Funtua 132kV

July 9, 2026
Auto Draft

DSS Ta Kama ‘Yar Jarida Zainab Sodiq Kan Zargin Mallakar Drone Ba Tare da Cikakkun Takardu ba

July 9, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji

July 9, 2026
Shaidar EFCC Ya Ce Sirika Bai Sanya Hannu A Takardun Kwangilar Naira Biliyan 2 Ba

Shaidar EFCC Ya Ce Sirika Bai Sanya Hannu A Takardun Kwangilar Naira Biliyan 2 Ba

July 9, 2026
’Yan Bindiga Sun Kashe Farfesa Har Lahira A  Jihar Benuwai

’Yan Bindiga Sun Kashe Farfesa Har Lahira A Jihar Benuwai

July 9, 2026
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane A Kaduna Da Filato

Sojoji Sun Hallaka Shugaban ’Yan Bindiga, Sun Daƙile Hare-hare A Zamfara

July 9, 2026
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

July 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.