A madadin kasar Sin mataimakin shugaban zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama’ar kasar Sin He Wei, ya ziyarci birnin Tehran na kasar Iran, domin halartar bikin jana’izar tsohon jagoran addinin kasar marigayi Ayatollah Ali Khamenei.
He Wei, ya kasance a kasar Iran a ranakun Alhamis da jiya Juma’a, inda ya gana da shugaban kasar Masoud Pezeshkian, da kakakin majalisar dokokin kasar Mohammad Baqer Qalibaf. Kazalika, ya gabatar da sakon ta’aziyya na kasar Sin, bisa rashin Khamenei, tare da bayyana matukar jaje ga gwamnati, da jama’ar Iran da ma daukacin iyalan Khamenei.
He Wei, ya kuma yi fatan karkashin jagorancin shugaban addini na kasar na yanzu Mojtaba Khamenei, Iran za ta farfado da tsaronta, da daidaito da gaggauta samar da ci gaba.
Bugu da kari, He ya ce Sin na maraba da sanya hannu da aka yi kan takardar fahimtar juna tsakanin Iran da Amurka, kana yana fatan sassan biyu za su aiwatar da sakamakon nasarorin da aka cimma, da wanzar da matakin tsagaita wuta, da aiwatar da tattaunawa mai ma’ana ta hakika, da ingiza karsashin gudanar da shawarwari.
Jami’in ya ce kasar Sin na fatan za a warware batun mashigin Hormuz yadda ya kamata, kana kasashen shiyyar za su kasance cikin yanayin lumana.
Da sanyin safiyar jiya Juma’a, manyan jami’an gwamnatin Iran, da jami’an gwamnatocin kasashen waje, sun ziyarci wurin da aka ajiye gawar marigayi Khamenei domin karrama shi, a wani bangare na bikin jana’izar da aka gudanar, a babban masallacin Imam Khomeini dake tsakiyar birnin Tehran. (Saminu Alhassan)













