ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

by El-Zaharadeen Umar
3 weeks ago

Gidauniyar Ɗahiru Bara’u Mangal ta bayyana cewa marasa lafiya masu ƙaramin ƙarfi sama da 30,000 ne suka amfana da shirye-shiryen ba da magani kyauta da ya gudanar a faɗin Jihar Katsina tun daga shekarar 2018.

Haka kuma, gidauniyar ta fara tantancewa da kula da kusan marasa lafiya 2,000 masu fama da cututtukan ido daban-daban, ciki har da waɗanda ke buƙatar tiyata.

Mamba a kwamitin amintattu na gidauniyar, Hussaini Kabir, ne ya bayyana hakan yayin ƙaddamar da shirin yi wa marasa lafiya sama da 700 tiyatar ƙumburin mara (Hernia) da kuma Hydrocele kyauta a babban asibitin Katsina.

ADVERTISEMENT

Kabir ya ce marasa lafiya sama da 700 daga sassa daban-daban na Jihar Katsina da ma wasu jihohi ne ake sa ran za su amfana da shirin tiyatar kyauta.

Ya bayyana cewa manufar shirin ita ce ƙara sauƙaƙa wa marasa ƙarfi samun ingantaccen kulawar lafiya.

LABARAI MASU NASABA

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

A cewarsa, ana fara tantance marasa lafiyar kafin a yi musu tiyata kyauta, yayin da waɗanda ke fama da ƙananan cututtuka za a ba su magunguna ba tare da sun biya komai ba.

“Shirin ana gudanar da shi lokaci-lokaci, kuma Alhaji Ɗahiru Bara’u Mangal ne ke ɗaukar nauyin komai domin samar da ingantaccen kulawar lafiya ga marasa galihu.

“Duk marasa lafiyar da ke buƙatar tiyata za a yi musu kyauta, yayin da waɗanda ke da ƙananan matsalolin lafiya za a ba su magungunan da suka dace ba tare da wani kuɗi ba,” in ji shi.

Kabir ya ƙara da cewa gidauniyar na kuma ɗaukar nauyin tiyatar ido kyauta, tiyatar cututtukan mafitsara da hanyoyin fitsari (urology), da sauran ayyukan jinya na musamman a faɗin Jihar Katsina. 

Shi ma da yake jawabi, Dakta Saifullahi Bawale ya yaba wa gidauniyar bisa yadda take taimaka wa gwamnati wajen inganta harkokin kiwon lafiya ta hanyar shirye-shiryen jinya kyauta.

Ya ce shirin ya dawo da fata ga dubban marasa ƙarfi da ba su da ikon biyan kuɗin magani.

A cewarsa, an tanadi isassun likitoci, ma’aikatan lafiya, kayan aiki, magunguna da sauran kayayyakin da ake buƙata domin tabbatar da nasarar shirin.

Wasu daga cikin waɗanda suka amfana da shirin sun gode wa gidauniyar, suna cewa tallafin ya sake ba su fata.

Malama Zulaihat Adamu daga ƙaramar hukumar Jibiya ta bayyana farin cikinta cewa ɗanta zai samu tiyatar Hernia kyauta, tana mai cewa sun daɗe ba su da ƙarfin biyan kuɗin maganin.

Shi ma Shamsu Abubakar ya yaba wa gidauniyar bisa ɗaukar nauyin tiyatar idonsa, tare da addu’ar Allah ya sa wannan ya zama ƙarshen matsalar idon da yake fama da ita.

Firdausi Muhammad daga ƙaramar hukumar Batsari ta ce shirin babban sauki ne ga marasa lafiya da ba za su iya biyan kuɗin tiyata ba, tare da yi wa wanda ya kafa gidauniyar addu’ar Allah ya ƙara masa albarka.

Rahotanni sun bayyana cewa gidauniyar na ci gaba da gudanar da shirin kula da lafiyar ido kyauta a cibiyar kula da Ido ta Katsina, inda ake tantancewa da ba marasa lafiya magani ba tare da biyan kuɗi ba.

Haka kuma, ana ba marasa lafiyar da ke buƙatar tabarau kyauta, yayin da waɗanda aka gano suna buƙatar tiyatar ido ake tsara musu ranar yin tiyatar ba tare da wani kuɗi ba.

El-Zaharadeen Umar
+ postsBio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Sana’ar Kilishi:Yadda Ta Bunkasa Daga Jihar Katsina Zuwa Wasu Sassan Nijeriya
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mutum 1,000 Daga Jam’iyyar ADC Sun Koma PDP A Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Tinubu Ya Amince Da Ɗaukar Ma’aikatan Gandun Daji 1,000 Domin Matsalolin Tsaro A Katsina

MASU ALAKA

Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa
Labarai

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

July 24, 2026
Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya
Ra'ayi Riga

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

July 24, 2026
NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci
Rahotonni

NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci

July 24, 2026
Next Post
Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

LABARAI MASU NASABA

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

July 24, 2026
Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

July 24, 2026
Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

July 24, 2026
An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

July 24, 2026
NNPP Za Ta Kwace Mulki A Jihar Imo – Kwankwaso

Jam’iyyar NDC Ta Shirya Tsaf Domin Kafa Gwamnati A 2027 —Kwankwaso

July 24, 2026
Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

July 24, 2026
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

July 24, 2026
Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

July 24, 2026
Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

July 24, 2026
Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

July 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.