ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

by El-Zaharadeen Umar
60 minutes ago

Gidauniyar Ɗahiru Bara’u Mangal ta bayyana cewa marasa lafiya masu ƙaramin ƙarfi sama da 30,000 ne suka amfana da shirye-shiryen ba da magani kyauta da ya gudanar a faɗin Jihar Katsina tun daga shekarar 2018.

Haka kuma, gidauniyar ta fara tantancewa da kula da kusan marasa lafiya 2,000 masu fama da cututtukan ido daban-daban, ciki har da waɗanda ke buƙatar tiyata.

Mamba a kwamitin amintattu na gidauniyar, Hussaini Kabir, ne ya bayyana hakan yayin ƙaddamar da shirin yi wa marasa lafiya sama da 700 tiyatar ƙumburin mara (Hernia) da kuma Hydrocele kyauta a babban asibitin Katsina.

ADVERTISEMENT

Kabir ya ce marasa lafiya sama da 700 daga sassa daban-daban na Jihar Katsina da ma wasu jihohi ne ake sa ran za su amfana da shirin tiyatar kyauta.

Ya bayyana cewa manufar shirin ita ce ƙara sauƙaƙa wa marasa ƙarfi samun ingantaccen kulawar lafiya.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

A cewarsa, ana fara tantance marasa lafiyar kafin a yi musu tiyata kyauta, yayin da waɗanda ke fama da ƙananan cututtuka za a ba su magunguna ba tare da sun biya komai ba.

“Shirin ana gudanar da shi lokaci-lokaci, kuma Alhaji Ɗahiru Bara’u Mangal ne ke ɗaukar nauyin komai domin samar da ingantaccen kulawar lafiya ga marasa galihu.

“Duk marasa lafiyar da ke buƙatar tiyata za a yi musu kyauta, yayin da waɗanda ke da ƙananan matsalolin lafiya za a ba su magungunan da suka dace ba tare da wani kuɗi ba,” in ji shi.

Kabir ya ƙara da cewa gidauniyar na kuma ɗaukar nauyin tiyatar ido kyauta, tiyatar cututtukan mafitsara da hanyoyin fitsari (urology), da sauran ayyukan jinya na musamman a faɗin Jihar Katsina. 

Shi ma da yake jawabi, Dakta Saifullahi Bawale ya yaba wa gidauniyar bisa yadda take taimaka wa gwamnati wajen inganta harkokin kiwon lafiya ta hanyar shirye-shiryen jinya kyauta.

Ya ce shirin ya dawo da fata ga dubban marasa ƙarfi da ba su da ikon biyan kuɗin magani.

A cewarsa, an tanadi isassun likitoci, ma’aikatan lafiya, kayan aiki, magunguna da sauran kayayyakin da ake buƙata domin tabbatar da nasarar shirin.

Wasu daga cikin waɗanda suka amfana da shirin sun gode wa gidauniyar, suna cewa tallafin ya sake ba su fata.

Malama Zulaihat Adamu daga ƙaramar hukumar Jibiya ta bayyana farin cikinta cewa ɗanta zai samu tiyatar Hernia kyauta, tana mai cewa sun daɗe ba su da ƙarfin biyan kuɗin maganin.

Shi ma Shamsu Abubakar ya yaba wa gidauniyar bisa ɗaukar nauyin tiyatar idonsa, tare da addu’ar Allah ya sa wannan ya zama ƙarshen matsalar idon da yake fama da ita.

Firdausi Muhammad daga ƙaramar hukumar Batsari ta ce shirin babban sauki ne ga marasa lafiya da ba za su iya biyan kuɗin tiyata ba, tare da yi wa wanda ya kafa gidauniyar addu’ar Allah ya ƙara masa albarka.

Rahotanni sun bayyana cewa gidauniyar na ci gaba da gudanar da shirin kula da lafiyar ido kyauta a cibiyar kula da Ido ta Katsina, inda ake tantancewa da ba marasa lafiya magani ba tare da biyan kuɗi ba.

Haka kuma, ana ba marasa lafiyar da ke buƙatar tabarau kyauta, yayin da waɗanda aka gano suna buƙatar tiyatar ido ake tsara musu ranar yin tiyatar ba tare da wani kuɗi ba.

El-Zaharadeen Umar
+ postsBio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mutum 1,000 Daga Jam’iyyar ADC Sun Koma PDP A Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Tinubu Ya Amince Da Ɗaukar Ma’aikatan Gandun Daji 1,000 Domin Matsalolin Tsaro A Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Matsalar Tsaro:Yadda Sabbin Matakan Gwamnati Ke Shafar Walwalar Al’ummar Jihar Katsina

MASU ALAKA

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

July 4, 2026
Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi
Labarai

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan
Labarai

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026
Next Post
Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

July 4, 2026
Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

July 4, 2026
Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

July 4, 2026
Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026
Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC

July 4, 2026
Gwamnan Katsina Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Cibiyar Gyaran Motoci Mai Amfani Da Hasken Rana

Gwamnan Katsina Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Cibiyar Gyaran Motoci Mai Amfani Da Hasken Rana

July 4, 2026
Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.