ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babban Editan LEADERSHIP, Azu, Ya Samu Lambar Yabo Ta NUJ Kan Ƙwarewar Aikin Jarida

by Sulaiman
2 months ago
Azu

Kungiyar ‘yan jarida ta Nijeriya (NUJ), reshen Babban Birnin Tarayya (FCT), ta zabi Babban Editan jaridar LEADERSHIP, Azu Ishiekwene, domin karbar lambar yabo ta ‘Media Leadership Excellence Award’ ta shekarar 2026.

 

An tsara wannan taron bayar da lambar yabo ne domin girmama ‘yan jarida da suka yi fice wajen nuna kwarewa, gaskiya, da kuma jajircewa wajen kiyaye ka’idojin aikin jarida mafi inganci.

ADVERTISEMENT
  • Taɓarɓarewar Sabis: NCC Ta Umarci Kamfanonin Sadarwa Su Biya Diyya
  • Tinubu Ya Ware Albashinsa Don Tallafa Wa Sojoji Da Iyalansu

A cikin wasikar nadin da Shugabar NUJ ta FCT, Grace Ike, da Shugaban Kwamitin Tsare-tsare, Obas Esiedesa, suka sanya wa hannu, kungiyar ta bayyana cewa an yi la’akari da kwarewar aiki, shaharar masana’antar yada labaran, da kuma tasirin aikin jarida ga al’umma wajen zaben wanda zai samu kyautar.

 

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

A cewar NUJ, an zabi Azu ne saboda gagarumar gudunmawar da ya bayar a aikin jarida, jajircewarsa wajen bin ka’idojin da’a, da kuma kokarinsa na yada labarai masu inganci, masu daidaito, kuma masu tasiri.

 

Wannan lambar yabo na daga cikin shirye-shiryen bikin Makon Jaridu na NUJ FCT na 2026, wanda za a gudanar a ranar Talata, 19 ga Mayu, 2026, a Abuja.

 

Ishiekwene na da kusan shekaru 40 yana aikin jarida. Mamba ne a Nigerian Guild of Editors (NGE), kuma ya taba zama shugaban kwamitin tantancewa na kyautar bayar da kyaututtuka ga hazikan ‘yan jarida na Afirka (CNN African Journalists of the Year).

 

Yana daya daga cikin wadanda suka kafa kungiyar Hadin Kan Editoci na Duniya (GEN), sannan ya taba zama mamba a kwamitin Dandalin Editoci na Duniya (WEF), kuma yana daga cikin fitattun marubutan sharhi a Afirka.

 

Ya rubuta littattafai da dama, ciki har da sabbi guda biyu da aka wallafa kwanan nan — ‘Writing for Media and Monetising It’, da ‘A Midlifer’s Guide to Content Creation and Profit’.

 

Haka kuma, shi ne shugaban Openfees, wata kungiya mai zaman kanta da ke biyan kudin makaranta ga daliban firamare da sakandare marasa galihu a Abuja.

 

Ya lashe lambobin yabo da dama, sannan yana koyarwa a matsayin dan sa-kai a tsohuwar makarantar sa, Sashen Mass Communication na Jami’ar jihar Legas.

Azu
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Mataimakin Shugaban Kasar Sin Ya Ziyarci Kasar Seychelles 

Mataimakin Shugaban Kasar Sin Ya Ziyarci Kasar Seychelles 

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.