ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babban Editan LEADERSHIP, Azu, Ya Samu Lambar Yabo Ta NUJ Kan Ƙwarewar Aikin Jarida

by Sulaiman
3 months ago
Azu

Kungiyar ‘yan jarida ta Nijeriya (NUJ), reshen Babban Birnin Tarayya (FCT), ta zabi Babban Editan jaridar LEADERSHIP, Azu Ishiekwene, domin karbar lambar yabo ta ‘Media Leadership Excellence Award’ ta shekarar 2026.

 

An tsara wannan taron bayar da lambar yabo ne domin girmama ‘yan jarida da suka yi fice wajen nuna kwarewa, gaskiya, da kuma jajircewa wajen kiyaye ka’idojin aikin jarida mafi inganci.

ADVERTISEMENT
  • Taɓarɓarewar Sabis: NCC Ta Umarci Kamfanonin Sadarwa Su Biya Diyya
  • Tinubu Ya Ware Albashinsa Don Tallafa Wa Sojoji Da Iyalansu

A cikin wasikar nadin da Shugabar NUJ ta FCT, Grace Ike, da Shugaban Kwamitin Tsare-tsare, Obas Esiedesa, suka sanya wa hannu, kungiyar ta bayyana cewa an yi la’akari da kwarewar aiki, shaharar masana’antar yada labaran, da kuma tasirin aikin jarida ga al’umma wajen zaben wanda zai samu kyautar.

 

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

A cewar NUJ, an zabi Azu ne saboda gagarumar gudunmawar da ya bayar a aikin jarida, jajircewarsa wajen bin ka’idojin da’a, da kuma kokarinsa na yada labarai masu inganci, masu daidaito, kuma masu tasiri.

 

Wannan lambar yabo na daga cikin shirye-shiryen bikin Makon Jaridu na NUJ FCT na 2026, wanda za a gudanar a ranar Talata, 19 ga Mayu, 2026, a Abuja.

 

Ishiekwene na da kusan shekaru 40 yana aikin jarida. Mamba ne a Nigerian Guild of Editors (NGE), kuma ya taba zama shugaban kwamitin tantancewa na kyautar bayar da kyaututtuka ga hazikan ‘yan jarida na Afirka (CNN African Journalists of the Year).

 

Yana daya daga cikin wadanda suka kafa kungiyar Hadin Kan Editoci na Duniya (GEN), sannan ya taba zama mamba a kwamitin Dandalin Editoci na Duniya (WEF), kuma yana daga cikin fitattun marubutan sharhi a Afirka.

 

Ya rubuta littattafai da dama, ciki har da sabbi guda biyu da aka wallafa kwanan nan — ‘Writing for Media and Monetising It’, da ‘A Midlifer’s Guide to Content Creation and Profit’.

 

Haka kuma, shi ne shugaban Openfees, wata kungiya mai zaman kanta da ke biyan kudin makaranta ga daliban firamare da sakandare marasa galihu a Abuja.

 

Ya lashe lambobin yabo da dama, sannan yana koyarwa a matsayin dan sa-kai a tsohuwar makarantar sa, Sashen Mass Communication na Jami’ar jihar Legas.

Azu
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
  • Sulaiman
    Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
  • Sulaiman
    Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

MASU ALAKA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
Next Post
Mataimakin Shugaban Kasar Sin Ya Ziyarci Kasar Seychelles 

Mataimakin Shugaban Kasar Sin Ya Ziyarci Kasar Seychelles 

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.