ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babban Editan LEADERSHIP, Azu, Ya Samu Lambar Yabo Ta NUJ Kan Ƙwarewar Aikin Jarida

by Sulaiman
5 months ago
Azu

Kungiyar ‘yan jarida ta Nijeriya (NUJ), reshen Babban Birnin Tarayya (FCT), ta zabi Babban Editan jaridar LEADERSHIP, Azu Ishiekwene, domin karbar lambar yabo ta ‘Media Leadership Excellence Award’ ta shekarar 2026.

 

An tsara wannan taron bayar da lambar yabo ne domin girmama ‘yan jarida da suka yi fice wajen nuna kwarewa, gaskiya, da kuma jajircewa wajen kiyaye ka’idojin aikin jarida mafi inganci.

ADVERTISEMENT
  • Taɓarɓarewar Sabis: NCC Ta Umarci Kamfanonin Sadarwa Su Biya Diyya
  • Tinubu Ya Ware Albashinsa Don Tallafa Wa Sojoji Da Iyalansu

A cikin wasikar nadin da Shugabar NUJ ta FCT, Grace Ike, da Shugaban Kwamitin Tsare-tsare, Obas Esiedesa, suka sanya wa hannu, kungiyar ta bayyana cewa an yi la’akari da kwarewar aiki, shaharar masana’antar yada labaran, da kuma tasirin aikin jarida ga al’umma wajen zaben wanda zai samu kyautar.

 

LABARAI MASU NASABA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

A cewar NUJ, an zabi Azu ne saboda gagarumar gudunmawar da ya bayar a aikin jarida, jajircewarsa wajen bin ka’idojin da’a, da kuma kokarinsa na yada labarai masu inganci, masu daidaito, kuma masu tasiri.

 

Wannan lambar yabo na daga cikin shirye-shiryen bikin Makon Jaridu na NUJ FCT na 2026, wanda za a gudanar a ranar Talata, 19 ga Mayu, 2026, a Abuja.

 

Ishiekwene na da kusan shekaru 40 yana aikin jarida. Mamba ne a Nigerian Guild of Editors (NGE), kuma ya taba zama shugaban kwamitin tantancewa na kyautar bayar da kyaututtuka ga hazikan ‘yan jarida na Afirka (CNN African Journalists of the Year).

 

Yana daya daga cikin wadanda suka kafa kungiyar Hadin Kan Editoci na Duniya (GEN), sannan ya taba zama mamba a kwamitin Dandalin Editoci na Duniya (WEF), kuma yana daga cikin fitattun marubutan sharhi a Afirka.

 

Ya rubuta littattafai da dama, ciki har da sabbi guda biyu da aka wallafa kwanan nan — ‘Writing for Media and Monetising It’, da ‘A Midlifer’s Guide to Content Creation and Profit’.

 

Haka kuma, shi ne shugaban Openfees, wata kungiya mai zaman kanta da ke biyan kudin makaranta ga daliban firamare da sakandare marasa galihu a Abuja.

 

Ya lashe lambobin yabo da dama, sannan yana koyarwa a matsayin dan sa-kai a tsohuwar makarantar sa, Sashen Mass Communication na Jami’ar jihar Legas.

Azu
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara
  • Sulaiman
    Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan
  • Sulaiman
    ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

MASU ALAKA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
Manyan Labarai

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa
Labarai

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
Next Post
Mataimakin Shugaban Kasar Sin Ya Ziyarci Kasar Seychelles 

Mataimakin Shugaban Kasar Sin Ya Ziyarci Kasar Seychelles 

LABARAI MASU NASABA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.