ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ambaliyar Ruwa: Gwamnati Ta Fara Kai Agajin Tan 12,000 Na Abinci Jigawa Da Anambra

by Sulaiman and Musa Muhammad
4 years ago
Ambaliyar ruwa

Gwamnatin Tarayya ta fara raba tan 12,000 na kayan abinci da wasu kayan da ba na abinci ba a jihohin da ambaliyar ruwa ta addabe su.

A ranar Juma’a aka kai wa Jihar Anambra wasu kayan da ba na abinci ba irin su tabarmin roba 7,350, gidan sauro 1,000, katan 600 na sabulun wanka, yadikan shadda 2,500 (kowanne yadi 5), sababbin tufafi na yara guda 1,000, sababbin tufafi na mata 1,000, da sababbin tufafi na maza 1,000.

  • Zamfarawa Na Alfahari Da Sadiya Umar Farouq – Gwamna Matawalle

Haka kuma za a kai wa jihar kayan abinci da su ka haɗa da buhun shinkafa 1,400, buhun wake 1,400 mai awon kilo 10, buhun masara 1,400 mai awon kilo 10, buhun gishiri 75 (awon kilo 20), jarkar man girki 75 (awon lita 20), katan 100 na magi da sauran su, da katan 75 na tumatirin kwali (sacat 50 cikin kowane katan).

ADVERTISEMENT

Ministar Harkokin Jinƙai, Agaji Da Inganta Rayuwa, Hajiya Sadiya Umar Farouq, ita ce ta bayyana wannan hoɓɓasan a jawabin ta a taron Ranar Rage Aukuwar Bala’o’i ta Duniya ta bana (2022 International Day for Disaster Risk Reduction) wanda aka yi a Abuja a ranar Juma’a.

Ministar, wadda ta samu wakilcin Daraktan Harkokin Agaji a ma’aikatar ta, Alhaji Ali Grema, ta ce ana ƙoƙarin a ƙara azama wajen tunkarar matsalolin ambaliya a ƙasar nan.

LABARAI MASU NASABA

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

Ta ce: “Duk dai ku na sane da ambaliya mai yawan gaske ta ke ta ragargazar jihohi da ƙananan hukumomi da garuruwa da dama a Nijeriya. Girman ɓarnar wannan ambaliya a ƙasar nan za a iya kwatanta shi ne kawai da ambaliyar da ta auku a cikin shekarar 2012.

“An yi asarar rayukan sama da mutum 500, kuma sama da mutum miliyan 1.4 abin ya shafa, kimanin gidaje 90,000 sun ruguje ko sashen su ya lalace, kuma bala’in na ci gaba.

“Haka kuma dubban hektocin gonaki sun lalace wanda hakan ya haifar da fargabar illata samar da abinci a ƙasar da ta fi kowace ƙasa yawan jama’a a Afrika. Wannan babban lamari ya shafi jihohi 27 a cikin jihohi 36 da Gundumar Birnin Tarayya da ake da su.

“A yayin da mu ke juyayin wannan yanayi na ambaliya a Nijeriya, ya kamata mu mai da hankali ga Cikakken Tsarin Rage Bala’i na 2022 (Inclusive Disaster Risk Reduction, IDDRR). Duk da yake ba za mu tsaya ɗora laifin kan wane ko wane ba, ya kamata ku amince da gaskiyar cewa dukkan mu mun samu isasshen gargaɗi kuma mun yi faɗakarwa da wuri.

“Sai dai, tilas ne jama’a su fahimci cewa kowane bala’i ya na faruwa ne a garuruwa kuma dole su riƙa ɗaukar rahotanni kan yanayi da gargaɗin kafin faruwar ambaliya da aka bayar da gaske.

“Ba za mu iya magance aukuwar ambaliya kwata-kwata ba amma za mu iya kare lafiyar jama’a. Haƙƙin yin hakan na mu duka ne.”

Ministar ta bayyana cewa ma’aikatar ta da dukkan masu ruwa da tsaki su na nan su na aikin aiwatar da Tsarin Agajin Gaggawa Ga Ambaliya na Ƙasa (National Flood Emergency Preparedness and Response Plan) wanda Majalisar Gudanarwa ta Tarayya ta amince da shi kwanan nan.

Hajiya Sadiya ta ce: “Tsarin ya gindaya wa dukkan jihohi da ƙananan hukumomi da ma gidaje da garuruwa da ƙungiyoyin sa ido ainihin aiki da kuma haƙƙin da ya rataya a wuyan kowannen su.

“Wannan ma’aikatar ta ɗauki aikin hana aukuwar mace-mace da rasa rayuka a lokacin aukuwar bala’i wanda ake ba da gargaɗi tun kafin faruwar sa kuma ya ke aukuwa a kowace shekara da muhimmanci.”

A wata hira da aka yi da shi, Darakta-Janar na Hukumar Agajin Gaggawa (NEMA), Mustapha Habib Ahmed, shi ma ya ba da tabbacin cewa an fara raba kayan agaji a sauran jihohi domin a rage wa mutanen da bala’in ambaliya ya shafa a jihohi 36 da Gundumar Birnin Tarayya.

Ya ce an fara rabon kayan ne daga Rumbun Musamman na Ƙasa ga mabuƙata a dukkan jihohi bisa amincewar Shugaba Muhammadu Buhari.

Ya ce: “NEMA ta riga ta kai kayan agaji ga jihohi da dama kuma ta miƙa su ga gwamnatocin jihohi daban-daban domin su raba wa mutanen da abin ya shafa.

“Mu na tabbatar wa da sauran jihohin da ba su karɓi nasu kayan agajin ba cewa kwanan nan za a gama kai wa nasu jihohin a cikin ƙarshen wannan makon. Ana ci gaba da ƙoƙarin tunkarar matsalolin da ake fama da su a lokacin kai kayan saboda yanayin hanyoyin da ambaliyar ruwan ta mamaye.

“Girman bala’in ambaliyar a faɗin ƙasar nan babba ne matuƙa. A yayin da sama da rayuka 500 su ka salwanta, an yi asarar gidaje da gonaki da dama, sannan tilas ɗimbin mutane sun bar gidajen su a wuraren da bala’in ya fi ta’azzara.”

Ambaliyar ruwa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Ambaliyar ruwa
Musa Muhammad
+ posts Bio
  • Musa Muhammad
    https://hausa.leadership.ng/author/musa-muhammad/
    “Babu Gaskiya A Takardar Da Ke Alaƙanta Gwamnatin Zamfara Da ’Yan Bindiga”
  • Musa Muhammad
    https://hausa.leadership.ng/author/musa-muhammad/
    Ina Rokon Allah Ya Sa Na Kammala Sana’ar Fim Cikin Mutunci – Jarumi Sadik
  • Musa Muhammad
    https://hausa.leadership.ng/author/musa-muhammad/
    Atiku Ga ‘Yan Inugu: Za Mu Samar Muku Da Romon Dimokraɗiyya Idan Kuka Zaɓe Mu
  • Musa Muhammad
    https://hausa.leadership.ng/author/musa-muhammad/
    2023: Atiku Ya Sha Alwashin Ƙara Wa Jihohi Da Ƙananan Hukumomi Ƙarfin Iko

MASU ALAKA

Ambaliyar ruwa
Rahotonni

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

May 17, 2026
Ambaliyar ruwa
Rahotonni

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

May 16, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Rahotonni

Almajiranci:Matsala Ko Maslaha

May 10, 2026
Next Post
Gunki Mafi Girma A Kasar Indonesia Ya Jawo Tarnaki

Gunki Mafi Girma A Kasar Indonesia Ya Jawo Tarnaki

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.