Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin Mao Ning, ta bayyana cewa, matakan Japan na fakewa da “barazanar waje” a matsayin hujjar fadada rundunar soja da shirin yaki, dabara ce ta rungumar ra’ayin nuna karfin soja. Kuma da zarar an fara aiwatar da ra’ayin nuna karfin soja, babu wanda zai iya ci gaba da kaucewa tasirin hakan.
Mao, ta bayyana hakan ne a yau Talata, a gun taron manema labarai na yau da kullum da aka gudanar, yayin da take mayar da martani ga kalaman da jami’an Japan suka furta a kwanan nan, game da gyara ka’idoji uku, masu nasaba da dawo da kayayyakin tsaro da Japan ke yi.
Dangane da kalaman ministan tsaron Philippines, game da Sin a taron tattaunawa kan aikin tsaro na Shangri-La kuwa, Mao ta bayyana cewa, shugaban Philippines ya yi ta ayyana aniyarsa ta magance bambance-bambance, da kuma inganta sassauta dangantakar kasar da bangaren Sin.
Ta ce ana fatan Philippines za ta daidaita kalamai da ayyukanta, kuma ta takaita kalamai da ayyukan jami’anta.Bugu da kari, dangane da sanarwar da Japan da Philippines suka fitar a kwanan nan, na kaddamar da tattaunawa game da kan iyakokin teku, Mao ta ce tattaunawar ta shafi tekun gabashin Taiwan, dole ne Sin ta shiga cikinta.
Japan da Philippines sun fara tattaunawa a game da iyakokin teku ba tare da Sin ba, wanda hakan ya saba wa dokokin kasa da kasa, da ka’idojin dangantakar kasa da kasa, kana ya yi matukar keta hakki da muradun Sin. Kuma Sin ba za ta amince da hakan ba. (Safiyah Ma)















Discussion about this post