Majalisar Dattawa ta Nijeriya a ranar Talata ta yi Allah-wadai da sace dalibai da malamai da aka yi a jihar Oyo, tana mai bayyana lamarin a matsayin mummunan hari kan martabar ‘yan kasa baki daya.
Wannan Allah-wadai ya zo ne yayin da majalisar ta koma zaman aiki bayan hutun Sallah, inda shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio, ya jagoranci sanatoci wajen yin tsayuwar minti guda domin girmama malamai biyu da wani dalibi da suka rasa rayukansu sakamakon harin.
Da yake jawabi ga sanatoci yayin zaman dawowa aiki, Akpabio ya ce sace daliban ya jefa kasar cikin bakin ciki tare da nuna bukatar gaggauta karfafa tsaro a makarantu da al’ummomi.
Ya ce, “Mun dawo bakin aiki ne cikin inuwa ta bakin ciki daga wata mummunar annoba da ta girgiza kasarmu. Sace dalibai da malamai a jihar Oyo ba wai hari ne kawai kan marasa laifi ba; hari ne kan martabar ‘yan kasar mu baki daya.”















Discussion about this post