ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Badaƙalar Kwangilar Sayen Magunguna A Kano: Da Wa Za Ta Bare?

by Abdullahi Muh'd Sheka and Sulaiman
2 years ago
Kano

Kamar yadda bayanai suka karade kafafen sada zumunta da dama kan batun badakalar kwangilar sayen maganguna ga kananan hukumomin Jihar Kano 44, wanda ya zama abin da ake ta cece-kuce a kansa, musamman ganin yadda shi jagoran gwamnatin Injiniya Abba Kabir Yusuf aka ji shi a wurin wani taro yana rantsuwa da Allah cewa duk wanda suka samu da hannu cikin kowacce irin badakala ba za su saurara masa ba. 

 

Cikin wadanda ake zargi na da hannu dumu-dumu har da dan’uwan jagoran Kwankwasiyya, Musa Garba Kwankwaso da kuma guda cikin makusancin gwamna wanda shi ne shugaban ma’aikatan fadar gwamnatin Jihar Kano, Shehu Wada Sagagi.

ADVERTISEMENT
  • Kaico: Wata Mata Ta Bankawa Kanta Wuta A Jigawa
  • Sin Ta Zama Zakaran Gwajin Dafi A Fannin Goyon Bayan Zaman Lafiya Da Adalci Tsakanin Kasashen Duniya

Wannan bankado badakalar ta tayar da hankalin Gwamnatin Kano, inda aka ji gwamna a cikin wata tattaunawa da shi yana bayyana cewa ba shi da masaniyar wannan harkalla, har sai da mai kwarmaton nan mazaunin kasar China, Dan Bello ya fallasa lamarin, wanda hakan tasa Gwamna Abba shan alwashin gudanar da bincike kan al’amarin.

 

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Kamar yadda bayanai ke nunawa, an yi kokarin kanface naira miliyon Goma-goma daga asusun a jiyar kowacce karamar hukuma cikin kananan hukumomin Jihar Kano 44, sannan ana ganin akwai sa hannu ko amincewar wasu kamar shugabannin kungiyar kananan hukumomin Jihar Kano, manyan daraktocin gudanarwar kananan hukumomi, daraktocin binciken ayyuka da tsare-tsaren kananan hukumomi, wanda ake ganin an kulla yadda aka yi amfani da kamfanin dan’uwan Kwankwaso, Garba Musa Kwankwaso mai suna ‘Nobomed Pharmaceuticals company.’

 

Babban abin da jama’a da sauran masu nazarin harkokin yau da kullum ke hange shi ne, shin an ya Hukumar Muhyi Magaji Rimin Gado za ta iya gudanar da sahihin bincike da zai kai ga hukunta duk wanda aka samu da hannu cikin wannan badakala, musamman ganin shi kansa shugaban hukumar da ke sauraron korafe-korafe ta kansa yake a halin yanzu, domin akwai korafe-korafe a kansa da ke gaban kotu.

 

Haka shi ma shugaban ma’aikatan fadar gwamnatin jihar, Shehu Wada Sagagi wanda cikin makonnin da suka gabata wasu fusatattun matasa suka afka wa wata makaranta da aka ce mallakarsa ce tare gano shinkafar da gwamnatin tarayya ta bayar domin raba wa al’umma wanda a jibge cikin makarantar, wanda haka tasa Sagagin garzayawa kotun, inda ya samo umarnin hana kamashi ko ci gaba da bincikarsa.

 

Da yawa mutane a Kano na kallon Gwamnatin Abba a matsayin gwamnatin dangi da abokan arziki, domin nade-naden da ke kunshe a cikinta ya nuna wasu da yawa na da alaka ta kusa ko ma ta jini da jagororin tafiyar, musamman an ga yadda watannin kadan da suka gabata aka nada dan Sanata Kwankwaso a matsayin Kwamishina, sannan akwai wasu masu fada aji a fadar gidan jagoran na Kwankwasiyya wadda ake ganin taba su na da wahalar gaske.

 

Hakan tasa ake ganin ba wata rawar a zo a gani da hukumar Muhyi Magaji za ta iya takawa wajen hukunta wadanda ake zargin cikin wannan badakala.

 

A wata tattaunawa da kamfanin dillancin labarai na Nijeriya (NAN) ta wayar tarho a Kano ranar Talata, an ji Muhyi Magaji na cewa, “Mun fara bincike mai zurfi kan zarge-zargen da ake yi game da samar da magunguna na biliyoyin naira ga kananan hukumomi 44.

 

Ya ce, “Duk wanda ke da hannu, za mu gano shi kuma za mu hukunta wadanda aka samu da laifi.”

 

A cewarsa, hukumar na binciken zargin karkatar da kayan abinci da aka yi wa shugaban ma’aikatan fadar gwamnatin Kano.

 

Kwamishinan yada labarai, Baba Halilu Dantiye da Darakta Janar na yada labaran gwamna, Sanusi Dawakin-Tofa ne suka sanya hannu a kan sanarwar.

 

Don haka gwamnan ya umurci hukumar da ta gaggauta fara bincike kan lamarin tare da kai rahoton sakamakon domin daukar matakin da ya dace.

 

Yanzu dai abin da aka jira a gani shi ne, yadda za ta kasance tsakanin hukumar Muhyi wanda shi kansa ake ganin na kasu da gwamnatin Abba ne, kuma gashi aiki ya biyo takansu, sannan kuma shi kansa yana da matsala a gaban kotu, ga kuma rantsuwar da gwamna ya yi na alkawarin ba zai daga wa duk wanda aka samu da almundahana kafa ba.

 

A halin da ake dai, Hukumar karbar koke-koke da yaki da cin hanci da rashawa ta Jihar Kano, ta kama wasu mutane biyar da suka hada da Alhaji Mohammed Kabara, babban sakataren ma’aikatar kananan hukumomi da masarautu, bisa zargin badakalar samar da magunguna na biliyoyin Naira.

 

Daga cikin wadanda aka kama akwai Garba Kwankwaso, Manajan Daraktan Kamfanin Magunguna na Nobomed, wanda dan uwa ne ga Shugaban Jam’iyyar NNPP na kasa, Sanata Rabi’u Kwankwaso

Maganguna
Abdullahi Muh'd Sheka
+ posts Bio
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Sakamakon Matsin Lambar Jami’an Tsaro, ‘Yan Ta’adda Na Fuskantar Ƙarancin Abinci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Kisan Gillar Mutum 7 A Kano: Sarakuna Da Malamai Da Iyaye Sun Nemi A Gaggauta Yanke Wa Waɗanda Ake Zargi Hukunci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    MACBAN Ta Nemi Amurka Ta Cire Sunanta Daga Jerin Waɗanda Ta Ƙaƙabawa Takunkumi
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo
Maganguna
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
PCACC Ta Kama Shugabannin Ƙananan Hukumomi 3 Bisa Zargin Almundahanar Miliyan 660

PCACC Ta Kama Shugabannin Ƙananan Hukumomi 3 Bisa Zargin Almundahanar Miliyan 660

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.