Tsohon gwamnan Jihar Kebbi kuma Ministan Kasafi da Tsare-tsaren Tattalin Arziki, Atiku Bagudu, ya jagoranci tawagar jam’iyyar APC daga jihar wajen miƙa fom ɗin nuna sha’awa da na tsayawa takara na gwamna Nasir Idris, domin neman tikitin jam’iyyar a karo na biyu a zaɓen 2027.
Matakin ya nuna kyakkyawar alaƙa tsakanin Bagudu da magajinsa, sabanin yadda ake yawan samun saɓani tsakanin tsoffin gwamnoni da waɗanda suka gaje su.
Da yake zantawa da manema labarai bayan miƙa fom ɗin, Bagudu ya ce jam’iyyar APC a matakin jiha da na ƙasa na bai wa ‘yan takara damar fafatawa cikin adalci, yana mai jaddada cewa tsarin jam’iyyar ya ba kowa dama ya nemi takara ba tare da takura ba.
Ya kuma yaba wa shugabancin jam’iyyar na ƙasa bisa tsawaita lokacin sayar da fom da miƙa su, domin bai wa masu sha’awar takara damar kammala shirye-shiryensu.
Bagudu ya ƙara da cewa irin wannan tsarin dimokuraɗiyya shi ne al’adar APC, inda ya tuna yadda Bola Ahmed Tinubu ya shiga zaɓen fidda gwani tare da sauran ‘yan takara a baya ba tare da wata takura ba.
Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da shirye-shiryen zaɓen 2027 ke ƙara ɗaukar zafi a sassa daban-daban na ƙasar.















Discussion about this post