ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bahallatsar Gabas Ta Tsakiya: Sin Da Pakistan Sun Ba Da Mafita

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 months ago
Sin

Fitinar da aka tayar a yankin Gabas ta Tsakiya ta addabi duniya, kuma babu abin da ake nema face mafita mai adalci da za ta kai ga samun dauwamammen zaman lafiya. Wannan ya sa kasar Sin da Pakistan suka gabatar da wata sahihiyar shawara da za ta zamo mafita ba kawai ga dakatar da yake-yake ba har ma da samun zaman lafiya mai dorewa a yankin Gulf da Gabas ta Tsakiya baki daya. Kowanne daga matakai biyar da shawarar ta kunsa, idan aka aiwatar da shi yadda ya dace, akwai yakinin zai karfafa dawo da kwanciyar hankali, saboda yana dauke da darussa daga tarihi wajen warware rikice-rikice da samar da zaman lafiya.

Mataki na farko shi ne dakatar da barin wuta nan da nan wanda yake nuni da kafa tubali na bin hanyar diflomasiyya. Tsagaita wuta na samar da yanayi mai kyau domin tattaunawa, da isar da kayan agaji, da kuma gina amincewa tsakanin bangarori masu dauki-ba-dadi. A tarihi, ana iya ganin tasirin haka a yakin Larabawa da Isra’ila a shekarar 1973, inda tsagaita wuta da Majalisar Dinkin Duniya ta jagoranta ya kawo karshen fada, ya kuma bude kofa ga yarjejeniyoyin sulhu.

Mataki na biyu shi ne fara tattaunawar sulhu da wuri-wuri wanda yake nuna cewa, amfani da karfin soji ba zai taba ba da mafita ba. Tattaunawa ita ce hanya mafi inganci wajen magance silar rikici, da warware sabani, da kuma samar da mafitar da kowa zai amince da ita. Yarjejeniyar Dayton ta 1995, wadda ta kawo karshen yakin Bosnia, daya ce daga misalan alfanun tattaunawa da wuri-wuri.

ADVERTISEMENT

Kazalika, daga matakan da shawarar ta gabatar, kiyaye barnata wuraren da ba na soja ba shi ne mataki na uku. Wannan yana da matukar muhimmanci, domin tabbatar da tsaron wuraren fararen hula kamar asibitoci, makarantu, da gidaje wajibi ne a karkashin dokokin kasa da kasa. Yarjejeniyoyin Geneva sun dade suna jaddada dokokin kare fararen hula, kuma aiwatar da su suna taimakawa sosai wajen rage asarar rayuka da dukiyoyin fararen hula.

Mataki na hudu shi ne kiyaye tsaron hanyoyin sufurin jiragen ruwa wanda tabbas ko makaho ya shafa, ya san wannan yana da matukar tasiri ba ga yankin Gulf da Gabas ta Tsakiya ba har ma ga duniya baki daya. Rufe mashigin Hormuz ya haifar da babbar tangarda ga zirga-zirgar jiragen ruwa musamman na dakon makamashi zuwa sassan duniya, don haka samar da wani hadin gwiwa mai adalci a bangaren sintiri zai taimaka ga samun zaman lafiya da habaka tattalin arziki.

LABARAI MASU NASABA

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Mataki na biyar da shawarar ta Sin da Pakistan ta gabatar shi ne girmama kundin tsarin Majalisar Dinkin Duniya wanda rashin yin hakan ne ya sa Amurka da Isra’ila suka yi gaban kansu wajen kaddamar da hari kan Iran, inda lamarin ya haifar da masifar da ake ciki a yankin. Kundin tsarin Majalisar Dinkin Duniya ya haramta keta ’yancin wata kasa, da yin katsalandan daga waje da kuma jaddada warware rikici ta hanyar zaman lafiya. Wannan ne yake ba kasashe damar magance matsaloli cikin adalci.

Hakika, duk da ana fuskantar kalubale musamman daga kasashe masu kunnen kashi, wannan shawara mai matakai biyar da Sin da Pakistan suka gabatar, mafita ce ga samar da zaman lafiya mai dorewa a Gabas ta Tsakiya. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe
  • Sulaiman
    GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara
  • Sulaiman
    Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026
  • Sulaiman
    Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

MASU ALAKA

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara
Daga Birnin Sin

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola
Daga Birnin Sin

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026
Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai
Daga Birnin Sin

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Next Post
Gwamnatin Borno Ta Nada Kwamitin Aiwatar Da Mafi Karancin Albashi

Zulum Ya Bayar Da Tallafin Naira Miliyan 150 Ga Iyalan Jami’an Soji Da Suka Rasu.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.