ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bahallatsar Gabas Ta Tsakiya: Sin Da Pakistan Sun Ba Da Mafita

by CGTN Hausa and Sulaiman
5 months ago
Sin

Fitinar da aka tayar a yankin Gabas ta Tsakiya ta addabi duniya, kuma babu abin da ake nema face mafita mai adalci da za ta kai ga samun dauwamammen zaman lafiya. Wannan ya sa kasar Sin da Pakistan suka gabatar da wata sahihiyar shawara da za ta zamo mafita ba kawai ga dakatar da yake-yake ba har ma da samun zaman lafiya mai dorewa a yankin Gulf da Gabas ta Tsakiya baki daya. Kowanne daga matakai biyar da shawarar ta kunsa, idan aka aiwatar da shi yadda ya dace, akwai yakinin zai karfafa dawo da kwanciyar hankali, saboda yana dauke da darussa daga tarihi wajen warware rikice-rikice da samar da zaman lafiya.

Mataki na farko shi ne dakatar da barin wuta nan da nan wanda yake nuni da kafa tubali na bin hanyar diflomasiyya. Tsagaita wuta na samar da yanayi mai kyau domin tattaunawa, da isar da kayan agaji, da kuma gina amincewa tsakanin bangarori masu dauki-ba-dadi. A tarihi, ana iya ganin tasirin haka a yakin Larabawa da Isra’ila a shekarar 1973, inda tsagaita wuta da Majalisar Dinkin Duniya ta jagoranta ya kawo karshen fada, ya kuma bude kofa ga yarjejeniyoyin sulhu.

Mataki na biyu shi ne fara tattaunawar sulhu da wuri-wuri wanda yake nuna cewa, amfani da karfin soji ba zai taba ba da mafita ba. Tattaunawa ita ce hanya mafi inganci wajen magance silar rikici, da warware sabani, da kuma samar da mafitar da kowa zai amince da ita. Yarjejeniyar Dayton ta 1995, wadda ta kawo karshen yakin Bosnia, daya ce daga misalan alfanun tattaunawa da wuri-wuri.

ADVERTISEMENT

Kazalika, daga matakan da shawarar ta gabatar, kiyaye barnata wuraren da ba na soja ba shi ne mataki na uku. Wannan yana da matukar muhimmanci, domin tabbatar da tsaron wuraren fararen hula kamar asibitoci, makarantu, da gidaje wajibi ne a karkashin dokokin kasa da kasa. Yarjejeniyoyin Geneva sun dade suna jaddada dokokin kare fararen hula, kuma aiwatar da su suna taimakawa sosai wajen rage asarar rayuka da dukiyoyin fararen hula.

Mataki na hudu shi ne kiyaye tsaron hanyoyin sufurin jiragen ruwa wanda tabbas ko makaho ya shafa, ya san wannan yana da matukar tasiri ba ga yankin Gulf da Gabas ta Tsakiya ba har ma ga duniya baki daya. Rufe mashigin Hormuz ya haifar da babbar tangarda ga zirga-zirgar jiragen ruwa musamman na dakon makamashi zuwa sassan duniya, don haka samar da wani hadin gwiwa mai adalci a bangaren sintiri zai taimaka ga samun zaman lafiya da habaka tattalin arziki.

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Mataki na biyar da shawarar ta Sin da Pakistan ta gabatar shi ne girmama kundin tsarin Majalisar Dinkin Duniya wanda rashin yin hakan ne ya sa Amurka da Isra’ila suka yi gaban kansu wajen kaddamar da hari kan Iran, inda lamarin ya haifar da masifar da ake ciki a yankin. Kundin tsarin Majalisar Dinkin Duniya ya haramta keta ’yancin wata kasa, da yin katsalandan daga waje da kuma jaddada warware rikici ta hanyar zaman lafiya. Wannan ne yake ba kasashe damar magance matsaloli cikin adalci.

Hakika, duk da ana fuskantar kalubale musamman daga kasashe masu kunnen kashi, wannan shawara mai matakai biyar da Sin da Pakistan suka gabatar, mafita ce ga samar da zaman lafiya mai dorewa a Gabas ta Tsakiya. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
  • Sulaiman
    Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
  • Sulaiman
    Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
  • Sulaiman
    Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

MASU ALAKA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
Daga Birnin Sin

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
Daga Birnin Sin

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Next Post
Gwamnatin Borno Ta Nada Kwamitin Aiwatar Da Mafi Karancin Albashi

Zulum Ya Bayar Da Tallafin Naira Miliyan 150 Ga Iyalan Jami’an Soji Da Suka Rasu.

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.