ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bahallatsar Gabas Ta Tsakiya: Sin Da Pakistan Sun Ba Da Mafita

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 months ago
Sin

Fitinar da aka tayar a yankin Gabas ta Tsakiya ta addabi duniya, kuma babu abin da ake nema face mafita mai adalci da za ta kai ga samun dauwamammen zaman lafiya. Wannan ya sa kasar Sin da Pakistan suka gabatar da wata sahihiyar shawara da za ta zamo mafita ba kawai ga dakatar da yake-yake ba har ma da samun zaman lafiya mai dorewa a yankin Gulf da Gabas ta Tsakiya baki daya. Kowanne daga matakai biyar da shawarar ta kunsa, idan aka aiwatar da shi yadda ya dace, akwai yakinin zai karfafa dawo da kwanciyar hankali, saboda yana dauke da darussa daga tarihi wajen warware rikice-rikice da samar da zaman lafiya.

Mataki na farko shi ne dakatar da barin wuta nan da nan wanda yake nuni da kafa tubali na bin hanyar diflomasiyya. Tsagaita wuta na samar da yanayi mai kyau domin tattaunawa, da isar da kayan agaji, da kuma gina amincewa tsakanin bangarori masu dauki-ba-dadi. A tarihi, ana iya ganin tasirin haka a yakin Larabawa da Isra’ila a shekarar 1973, inda tsagaita wuta da Majalisar Dinkin Duniya ta jagoranta ya kawo karshen fada, ya kuma bude kofa ga yarjejeniyoyin sulhu.

Mataki na biyu shi ne fara tattaunawar sulhu da wuri-wuri wanda yake nuna cewa, amfani da karfin soji ba zai taba ba da mafita ba. Tattaunawa ita ce hanya mafi inganci wajen magance silar rikici, da warware sabani, da kuma samar da mafitar da kowa zai amince da ita. Yarjejeniyar Dayton ta 1995, wadda ta kawo karshen yakin Bosnia, daya ce daga misalan alfanun tattaunawa da wuri-wuri.

ADVERTISEMENT

Kazalika, daga matakan da shawarar ta gabatar, kiyaye barnata wuraren da ba na soja ba shi ne mataki na uku. Wannan yana da matukar muhimmanci, domin tabbatar da tsaron wuraren fararen hula kamar asibitoci, makarantu, da gidaje wajibi ne a karkashin dokokin kasa da kasa. Yarjejeniyoyin Geneva sun dade suna jaddada dokokin kare fararen hula, kuma aiwatar da su suna taimakawa sosai wajen rage asarar rayuka da dukiyoyin fararen hula.

Mataki na hudu shi ne kiyaye tsaron hanyoyin sufurin jiragen ruwa wanda tabbas ko makaho ya shafa, ya san wannan yana da matukar tasiri ba ga yankin Gulf da Gabas ta Tsakiya ba har ma ga duniya baki daya. Rufe mashigin Hormuz ya haifar da babbar tangarda ga zirga-zirgar jiragen ruwa musamman na dakon makamashi zuwa sassan duniya, don haka samar da wani hadin gwiwa mai adalci a bangaren sintiri zai taimaka ga samun zaman lafiya da habaka tattalin arziki.

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

Mataki na biyar da shawarar ta Sin da Pakistan ta gabatar shi ne girmama kundin tsarin Majalisar Dinkin Duniya wanda rashin yin hakan ne ya sa Amurka da Isra’ila suka yi gaban kansu wajen kaddamar da hari kan Iran, inda lamarin ya haifar da masifar da ake ciki a yankin. Kundin tsarin Majalisar Dinkin Duniya ya haramta keta ’yancin wata kasa, da yin katsalandan daga waje da kuma jaddada warware rikici ta hanyar zaman lafiya. Wannan ne yake ba kasashe damar magance matsaloli cikin adalci.

Hakika, duk da ana fuskantar kalubale musamman daga kasashe masu kunnen kashi, wannan shawara mai matakai biyar da Sin da Pakistan suka gabatar, mafita ce ga samar da zaman lafiya mai dorewa a Gabas ta Tsakiya. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
Gwamnatin Borno Ta Nada Kwamitin Aiwatar Da Mafi Karancin Albashi

Zulum Ya Bayar Da Tallafin Naira Miliyan 150 Ga Iyalan Jami’an Soji Da Suka Rasu.

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.