Rahotanni sun ce wasu ɓata-gari sun kai wa ayarin motocin ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NDC, Peter Obi hari, a ranar Talata a Jihar Benue.
Lamarin ya faru ne a kan titin Gboko zuwa Makurdi, yayin da Obi ke kan hanyarsa ta zuwa Yelwata, Ƙaramar Hukumar Guma, domin ziyartar waɗanda harin ranar 13 ga watan Yuni, 2025 ya shafa.
Sakataren Yaɗa Labarai na NDC a Benue, Agile Bem Ordedoo, ya zargi jam’iyyar APC da tura ɓata-gari domin hana Obi isa Yelwata.
Ya ce Obi ya shirya zuwa domin jajanta wa waɗanda abin ya shafa tare da kai musu tallafi.
Sai dai Sakataren Yaɗa Labarai na APC a Benue, Benedict Yaweh, ya musanta zargin.
Ya ce jam’iyyar ba ta da masaniya kan harin, kuma idan har lamarin ya faru, mai yiwuwa wasu magoya bayan jam’iyyar da suka fusata ne suka kai hari ba ’yan APC ba.
Harin da aka kai Yelwata a ranar 13 ga watan Yuni, 2025 ya yi sanadin mutuwar mutane da dama tare da tilasta wasu mazauna yankin tserewa daga gidajensu.
Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoton, ’yansanda ba su tabbatar da faruwar harin ba, domin kakakin rundunar bai amsa kiran waya da aka yi masa ba.














