ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bambancin Sin Da Amurka Bai Tsaya Kan Manufofi Kadai Ba

by Sulaiman
2 months ago
Amurka

Jaridar “The Hill” ta kasar Amurka, ta wallafa wani bayani a kwanan nan, mai taken “Kasar Sin ta samar da tabbaci ga kasashen Afirka, yayin da kasar Amurka ta kayyade musu wa’adi kadai”. Inda marubucin bayanin ya kwatanta manufofin ciniki na kasashen Amurka da Sin, yana mai cewa, kasar Amurka ta bar dokarta da ta shafi yafe wa wasu kasashen dake nahiyar Afirka harajin kwastam ta AGOA, ta zama mai zarce wa’adi, sa’an nan ko da yake ta tsawaita wa’adin dokar da shekara daya, amma ta sanya kasashen Afirka biyan karin harajin kwastam na kaso 15. Yayin da a nata bangare, kasar Sin ta yi alkawarin yafe wa dukkan kasashe 53 dake nahiyar Afirka da suka kulla huldar diflomasiyya da ita harajin kwastam.

Ganin haka ya sa marubucin ya shawarci kasar Amurka da ta daidaita manufar ciniki a kokarin “takara da kasar Sin”, domin a ganinsa muddin kasar Amurka ta gyara wasu manufofinta, to, za ta zama mai samun karbuwa kamar yadda kasar Sin take a Afirka. Sai dai a hakika, bambancin kasashen Sin da Amurka bai tsaya ne kan wasu manufofi kadai ba, har ma ya shafi wasu manyan akidu nasu.

Wani shehun malami dake aiki a jami’ar Harvard ta kasar Amurka, mai suna Stephen Walt, ya ce babbar akidar kasar Amurka ita ce zama mai kwatar dukiyoyi da albarkatu, da aiwatar da mulkin danniya a duniya. Wannan ra’ayi ya sa kasar son daukar matakan kashin kai, da nuna son kai da girman kai, da kokarin cin zarafin sauran kasashe. Zuwa yanzu, kasar Amurka ta janye jikinta daga kungiyoyin kasa da kasa 66, da karbar karin harajin kwastam kan kayayyakin sauran kasashe yadda ta ga dama. Sa’an nan, a kwanan baya, kasar Amurka ta far wa kasar Venezuela, da matsawa kasar Cuba lamba, tare da haifar da tashin hankali a yankin Latin Amurka, kafin daga bisani ta hada kai da kasar Isra’ila wajen kai hare-hare kan kasar Iran, inda ta haddasa bala’in jin kai, da haifar da matsala ga zirga-zirgar jiragen ruwa ta shigar teku ta Hormuz, da kuma girgizar farashin mai a kasuwannin duniya.

ADVERTISEMENT

A nata bangare, akidar da kasar Sin ta dauka akasin ta kasar Amurka ce. Yayin da duniyarmu ke fuskantar wani yanayi na tangal-tangal, kasar Sin tana tsayawa tsayin daka kan yunkurin tabbatar da zaman lafiya da ci gaban tattalin arziki. A shekarun nan, kasar Sin ta gabatar da dimbin shawarwari masu muhimmanci, da suka shafi samar da ci gaban tattalin arziki, da tsaro a duniya, da kare al’adun gargajiya, da kula da al’amuran kasa da kasa yadda ya kamata. Kana a kokarin tinkarar tashin hankalin da ake fuskantar yanzu a yankin Gabas ta Tsakiya, kasar Sin ta shiga aikin sulhunta bangarori masu ruwa da tsaki, da neman daidaita lamarin karkashin tsarin Majalisar Dinkin Duniya, har ma ta hada hannu da kasar Pakistan wajen gabatar da wasu shawarwarin tabbatar da zaman lafiya, a kokarin daidaita rikicin da ake fuskantar.

Wannan bambancin ra’ayin dake tsakanin kasashen Sin da Amurka ya haifar da sakamako: kamar yadda wani sakamakon bincike da kamfanin Gallup mai gudanar da binciken ra’ayin jama’a na kasar Amurka ya gabatar a kwanan baya ya nuna, cewa yawan mutanen kasashe daban daban da suka yarda da kwarewar kasar Sin a fannin jagoranci a duniya ya kai kaso 36 a shekarar 2025, yayin da jimillar da kasar Amurka ta samu ita ce kaso 31. Inda wannan bambanci na kaso 5 ya zama mafi girma cikin dukkan sakamakon binciken da kamfanin Gallup ya gudanar cikin shekaru 20 da suka gabata.

LABARAI MASU NASABA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”

Dalilin da ya sa ake samun bambanci wajen amincewa tsakanin kasashen Sin da Amurka, shi ne kasashen biyu na rungumar akidu daban daban, inda akidar Amurka ita ce mulkin danniya, da tabbatar da moriyar kai da faduwar wani, yayin da ra’ayin da kasar Sin ke tsayawa a kai shi ne, barin bangarori daban daban su yi shawarwari, da tabbatar da moriyar dukkan bangarori, da neman ci gaban tattalin arziki da tabbatar da zaman lafiya a lokaci guda. Ko shakka babu ra’ayin kasar Sin shi ne mai samun karbuwa da amincewa daga al’ummun duniya. (Bello Wang)

Amurka
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
  • Sulaiman
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili
  • Sulaiman
    Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa
  • Sulaiman
    Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

MASU ALAKA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci
Ra'ayi Riga

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”

June 12, 2026
Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 
Ra'ayi Riga

Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 

June 10, 2026
Next Post
Dalilin Da Ya Sa Sabon Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Jihar Mongoliya Ta Gida Ke Jawo Hankalin Duniya

Dalilin Da Ya Sa Sabon Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Jihar Mongoliya Ta Gida Ke Jawo Hankalin Duniya

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.