Jaridar “The Hill” ta kasar Amurka, ta wallafa wani bayani a kwanan nan, mai taken “Kasar Sin ta samar da tabbaci ga kasashen Afirka, yayin da kasar Amurka ta kayyade musu wa’adi kadai”. Inda marubucin bayanin ya kwatanta manufofin ciniki na kasashen Amurka da Sin, yana mai cewa, kasar Amurka ta bar dokarta da ta shafi yafe wa wasu kasashen dake nahiyar Afirka harajin kwastam ta AGOA, ta zama mai zarce wa’adi, sa’an nan ko da yake ta tsawaita wa’adin dokar da shekara daya, amma ta sanya kasashen Afirka biyan karin harajin kwastam na kaso 15. Yayin da a nata bangare, kasar Sin ta yi alkawarin yafe wa dukkan kasashe 53 dake nahiyar Afirka da suka kulla huldar diflomasiyya da ita harajin kwastam.
Ganin haka ya sa marubucin ya shawarci kasar Amurka da ta daidaita manufar ciniki a kokarin “takara da kasar Sin”, domin a ganinsa muddin kasar Amurka ta gyara wasu manufofinta, to, za ta zama mai samun karbuwa kamar yadda kasar Sin take a Afirka. Sai dai a hakika, bambancin kasashen Sin da Amurka bai tsaya ne kan wasu manufofi kadai ba, har ma ya shafi wasu manyan akidu nasu.
Wani shehun malami dake aiki a jami’ar Harvard ta kasar Amurka, mai suna Stephen Walt, ya ce babbar akidar kasar Amurka ita ce zama mai kwatar dukiyoyi da albarkatu, da aiwatar da mulkin danniya a duniya. Wannan ra’ayi ya sa kasar son daukar matakan kashin kai, da nuna son kai da girman kai, da kokarin cin zarafin sauran kasashe. Zuwa yanzu, kasar Amurka ta janye jikinta daga kungiyoyin kasa da kasa 66, da karbar karin harajin kwastam kan kayayyakin sauran kasashe yadda ta ga dama. Sa’an nan, a kwanan baya, kasar Amurka ta far wa kasar Venezuela, da matsawa kasar Cuba lamba, tare da haifar da tashin hankali a yankin Latin Amurka, kafin daga bisani ta hada kai da kasar Isra’ila wajen kai hare-hare kan kasar Iran, inda ta haddasa bala’in jin kai, da haifar da matsala ga zirga-zirgar jiragen ruwa ta shigar teku ta Hormuz, da kuma girgizar farashin mai a kasuwannin duniya.
A nata bangare, akidar da kasar Sin ta dauka akasin ta kasar Amurka ce. Yayin da duniyarmu ke fuskantar wani yanayi na tangal-tangal, kasar Sin tana tsayawa tsayin daka kan yunkurin tabbatar da zaman lafiya da ci gaban tattalin arziki. A shekarun nan, kasar Sin ta gabatar da dimbin shawarwari masu muhimmanci, da suka shafi samar da ci gaban tattalin arziki, da tsaro a duniya, da kare al’adun gargajiya, da kula da al’amuran kasa da kasa yadda ya kamata. Kana a kokarin tinkarar tashin hankalin da ake fuskantar yanzu a yankin Gabas ta Tsakiya, kasar Sin ta shiga aikin sulhunta bangarori masu ruwa da tsaki, da neman daidaita lamarin karkashin tsarin Majalisar Dinkin Duniya, har ma ta hada hannu da kasar Pakistan wajen gabatar da wasu shawarwarin tabbatar da zaman lafiya, a kokarin daidaita rikicin da ake fuskantar.
Wannan bambancin ra’ayin dake tsakanin kasashen Sin da Amurka ya haifar da sakamako: kamar yadda wani sakamakon bincike da kamfanin Gallup mai gudanar da binciken ra’ayin jama’a na kasar Amurka ya gabatar a kwanan baya ya nuna, cewa yawan mutanen kasashe daban daban da suka yarda da kwarewar kasar Sin a fannin jagoranci a duniya ya kai kaso 36 a shekarar 2025, yayin da jimillar da kasar Amurka ta samu ita ce kaso 31. Inda wannan bambanci na kaso 5 ya zama mafi girma cikin dukkan sakamakon binciken da kamfanin Gallup ya gudanar cikin shekaru 20 da suka gabata.
Dalilin da ya sa ake samun bambanci wajen amincewa tsakanin kasashen Sin da Amurka, shi ne kasashen biyu na rungumar akidu daban daban, inda akidar Amurka ita ce mulkin danniya, da tabbatar da moriyar kai da faduwar wani, yayin da ra’ayin da kasar Sin ke tsayawa a kai shi ne, barin bangarori daban daban su yi shawarwari, da tabbatar da moriyar dukkan bangarori, da neman ci gaban tattalin arziki da tabbatar da zaman lafiya a lokaci guda. Ko shakka babu ra’ayin kasar Sin shi ne mai samun karbuwa da amincewa daga al’ummun duniya. (Bello Wang)















Discussion about this post