ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bangare Japan Da Ya Dage Sai Ya Zubar Da Dagwalon Ruwan Nukiliya Cikin Teku Zai Sha Kunya Ta Tsawon Tarihi

by CMG Hausa
3 years ago
The Joban Joint Power Co. Nakoso thermal power station, rear, in Iwaki, Fukushima Prefecture, Japan, on Tuesday, July 4, 2023. Japanese utility Tepco is planning to release more than 1 million cubic meters of treated radioactive water — enough to fill 500 Olympic-size swimming pools — from the wrecked Fukushima Dai-Ichi nuclear power plant into the Pacific Ocean, part of its nearly $150 billion effort to clean up the worst atomic accident since Chernobyl. Photographer: Soichiro Koriyama/Bloomberg

The Joban Joint Power Co. Nakoso thermal power station, rear, in Iwaki, Fukushima Prefecture, Japan, on Tuesday, July 4, 2023. Japanese utility Tepco is planning to release more than 1 million cubic meters of treated radioactive water — enough to fill 500 Olympic-size swimming pools — from the wrecked Fukushima Dai-Ichi nuclear power plant into the Pacific Ocean, part of its nearly $150 billion effort to clean up the worst atomic accident since Chernobyl. Photographer: Soichiro Koriyama/Bloomberg

A ranar 7 ga wata, Hukumar Kula da Makamshin Nukiliya ta Japan, ta ba da takardar shaidar amincewa da na’urorin zubar da dagwalon ruwan nukiliya na Fukushima, ga Kamfanin Wutar Lantarki na Tokyo. Hakan na nufin gwamnatin Japan ta kara daukar wani mataki na shirin zubar da dagwalon ruwan nukiliyar cikin teku, duk da tsananin adawa da hakan ke fuskanta a cikin gida da waje.

Kungiyoyin fararen hula da dama a jihar Fukushima, da sauran wuraren kasar sun sanar a wannan rana cewa, mutane 254,000, sun rattaba hannu kan adawa da wannan shirin. Wani binciken hadin gwiwa da kafafen yada labarai na Japan, da Koriya ta Kudu suka gudanar, ya nuna cewa, sama da kashi 80% na al’ummar Koriya ta Kudu, ba su amince da shirin na Japan ba.

  • Sin Ta Bukaci Japan Da Kada Ta Yi Yunkurin Amfani Da Rahoton IAEA A Matsayin Izinin Zubar Da Dagwalon Ruwan Nukiliya A Cikin Teku

Kaza lika jama’a a kasashen tsibiran tekun Pasifik, da Philippines, da Indonesia, da Afirka ta Kudu, da Peru, da sauran kasashe da dama, sun yi korafi game da wannan batu a ’yan kwanakin nan. Hakan na nuni da cewa, matakin da kasar Japan ta dauka na zubar da dagwalon ruwan nukiliya a cikin teku, wanda ya saba wa ra’ayin al’ummar duniya, bai samu amincewa ba.

ADVERTISEMENT

Bugu da kari, sakamakon wasu kuri’un jin ra’ayin al’umma guda 2 da kafar CGTN ta gudanar ta yanar gizo sun nuna cewa, kaso 94.85 bisa dari na wadanda suka amsa tambayoyi sun yi Allah wadai da matakin kasar Japan, suna masu bayyana shi a matsayin tsananin rashin sanin ya kamata, kana karin wasu kaso 3.64 bisa dari kwatankwacin na watanni 3 da suka gabata. Yanzu haka dai sassan kasashen duniya na ta kara nuna damuwa ga matakin da Japan din ke burin aiwatarwa.

Wannan bincike, wanda kafar CGTN ta fitar ta tashoshin ta na Turanci, da Faransanci da Larabci, da yarukan Sipaniya da na Rasha, ya samu amsoshi daga mutane kusan 34,000 cikin sa’o’i 24.

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Domin tsimin kudi, Japan tana daukar tekun Pasifik a matsayin magudanar ruwa, wanda hakan zai rataya mata diyyar kasashen duniya ta fuskokin da’a da sanin ya kamata.

Idan har Japan ta dage sai ta zubar da dagwalon ruwan nukiliyar ta cikin teku, to tabbas hakan zai sanya ta jin kunya ta tsawon tarihi. (Masu Fassarawa: Bilkisu Xin, Saminu Alhassan)

Japan
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
Sharhi: Sin Da Amurka Ba Su Bukatar Zama Abokan Gabar Juna 

Sharhi: Sin Da Amurka Ba Su Bukatar Zama Abokan Gabar Juna 

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.