Babban jami’in tawagar dindindin ta kasar Sin a MDD Teng Fei, ya jaddada matsayar Sin cewa, “tsarin kafa kasashe biyu” shi ne hanya daya tilo da za a iya bi don magance matsalar Palasdinu.Teng Fei ya bayyana hakan ne a jiya Juma’a, yayin taron kwamitin sulhun MDD kan halin da ake ciki a gabar yammacin kogin Jordan, inda ya ce a kwanan nan, halin da ake ciki a yankin na kara ta’azzara, kuma tashe-tashen hankula da suka sabawa doka na kara yawaita.
A daya bangaren matsalar Palasdinu, ta dade tana gudana a tsawon shekaru.Ya ce kwamitin sulhu, da babban taron MDD sun riga sun zartar da kudurori da yawa, kuma kotun duniya ta bayar da shawarwari kan batun mamayar, amma dalilin da ya sa halin da ake ciki ke da wahalar gyara, shi ne an kasa aiwatar da shawarwarin da suka dace.
Ya ce kamata ya yi al’ummun kasa da kasa su dauki matakai da suka dace, su gaggauta maido da kwanciyar hankali a gabar yammacin kogin Jordan, da kuma ciyar da matsalar Palasdinu gaba, domin samun cikakkiyar mafita mai adalci da dorewa cikin gaggawa.
Teng Fei ya ce, bangaren Sin yana son yin hadin kai da al’ummun kasa da kasa, wajen yin kokari ba tare da tsayawa ba, don kawo karshen wahalar da al’ummar Palasdinu ke ciki, da aiwatar da “tsarin kasashe biyu”, da kuma cimma zaman lafiya da hadin kai tsakanin Palasdinu da Isra’ila. (Mai Fassara: Amina Xu)















Discussion about this post