Shugaba Donald Trump, a ranar Litinin, ya yi gargaɗin cewa duk wata ƙasa da ke hulda da Iran za ta fuskanci harajin kaso 25 cikin 100 kan duk wani ciniki da Amurka.
A cikin wata sanarwa da ya fitar a shafinsa na sada zumunta da aka tabbatar, Trump ya ce, “Daga yau, duk kasar da ke hulda da Jamhuriyar Musulunci ta Iran za ta biya harajin kaso 25% kan duk wani kasuwanci da take yi da Amurka.”
- Gwamnan Gombe Ya Yi Ta’aziyyar Mutane 5 Da Suka Rasu A Hatsarin Mota
- Huldar Dake Tsakanin Sin Da Afirka Na Kara Yaukaka
Wannan karin harajin dai, ya shafi kasashe ne da ke shigar da kayayyakinsu zuwa kasar Amurka. Iran, mamba ce a kungiyar kasashe masu samar da mai a duniya (OPEC), ta shafe shekaru tana fuskantar takunkumi mai tsanani daga Amurka, amma ta kan iya fitar da yawancin manta zuwa China.
Turkiyya, Iraki, UAE da Indiya suma suna cikin manyan abokan huldar cinikayya da Iran.
A ‘yan kwanakin nan, Iran ta fuskanci zanga-zanga mai muni kan tsadar rayuwa wacce ta rikiɗe ta koma adawa da gwamnati, inda aka yi asarar rayuka da ababen more rayuwa, wacce ta yi barazanar sauya gwamnatin kasar amma a jiya Litinin, a iya cewa, gwamnatin Iran ta shawo kan wannan kalubale bayan da miliyoyin jama’a a Tehran da wasu manyan biranen kasar suka fito don nuna goyon bayansu ga gwamnati.
Amurka dai, ta sha alwashin kai hare-hare idan Iran ta muzgunawa masu zanga-zangar, amma daga karshe, a iya cewa, batun zanga-zanga ya zama tarihi.
ADVERTISEMENT















Discussion about this post