Mutane biyar sun rasu sakamakon hatsarin mota da ya auku biyo bayan fashewa da wata tanka ta yi a garin Lawanti, ƙaramar hukumar Akko, Jihar Gombe a ranar Lahadi.
Waɗanda suka rasu sun haɗa da Babayo Bello Konkeje (60), Ahmadu Adamu Konkeje (43), Yahaya M. Manu Konkeje (40), Haruna Abdu Shulto (45), da Yana Alhaji Jarami Dunumari (51). Wasu da dama kuma sun ji rauni.
- An Kama Bokan Da Ya Yi Wa Mali Alƙawarin Lashe Gasar AFCON Ta 2025
- ’Yan Bindiga Sun Kashe Manomi, Sun Tilasta Wa Mazauna Ƙauyuka Tserewa A Benue
Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ya halarci jana’izar mamatan, inda ya bayyana lamarin a matsayin “babban rashi” ga jihar.
Ya yi ta’aziyya ga iyalan waɗanda suka rasu da al’ummar Lawanti, inda ya kuma tuna da mutane bakwai daga Lawanti da suka mutu a wani hatsari daban a watan Disamban 2025.
Gwamnan ya yi mamatan addu’a da neman gafara, ya yi alƙawarin daukar matakai don hana faruwar irin wannan hatsari a nan gaba, sannan ya bayar da Naira miliyan biyar don tallafa wa iyalansu.
Mai Unguwar Lawanti, Alhaji Bello Hassan, ya gode wa gwamnan kan halartar jana’izar da tallafin da ya bayar.















Discussion about this post