Daga ranar Laraba da ta gabata zuwa jiya Litinin, Wang Yi, ministan harkokin wajen kasar Sin ya kai ziyara hedkwatar kungiyar tarayyar Afirka ta AU, da kasashen Habasha, da Tanzania, da Lesotho, daya bayan daya. Ziyararsa ta sake tabbatar da al’adar kasar Sin a fannin diplomasiyya, wato ministan wajen kasar ya kan kai ziyara nahiyar Afirka a farkon duk shekara. Hakika kasar Sin ta riga ta kiyaye wannan al’ada har tsawon shekaru 36.
Minista Wang Yi ya yi tsokaci kan dalilin kasar Sin na kiyaye wannan al’ada, inda ya ce, kasar Sin da kasashen Afirka suna da abokantaka mai zurfi da dogon tarihi, don haka, a ganin kasar Sin, ya kamata ta karfafa wannan hulda da kasashen Afirka a farkon duk shekara, kamar dai yadda wani mutum ke mika gaisuwa da fatan alheri ga ’yan uwansa, gami da ziyartar gidajensu a bikin sabuwar shekara. A zahiri, wannan ziyara da mista Wang Yi ya yi, ta nuna dorewar manufar kasar Sin ta fuskar hulda da kasashen Afirka, da hadin kan kasashe masu tasowa a duniya, gami da aza harsashi ga karin hadin gwiwar bangarorin Sin da Afirka a shekarar da muke ciki.
A yayin ziyararsa a nahiyar Afirka, ministan wajen kasar Sin Wang Yi ya jagoranci taron tattaunawar bangarorin Sin da Afirka kan manyan tsare-tsare, a hadin gwiwarsa da Mahmoud Youssouf, shugaban kwamitin kungiyar AU, inda dukkan bangarorin 2 suka jaddada bukatar karfafa karfi a kokarin kare hakkin Sin da Afirka, da tabbatar da zaman lafiya da ci gaba a duniya. Ban da haka, jami’an 2 sun gane ma idanunsu yadda aka kaddamar da Shekarar Cudanyar Al’ummun Sin Da Afirka, inda a karkashin wannan take, za a gudanar da shirye-shirye kusan 600 da suka shafi harkokin matasa, da ta al’adu, da hadin gwiwar kafofin watsa labaru, da dai sauransu, tsakanin bangarorin Sin da Afirka, a shekarar 2026.
Watakila za ka so sanin dalilin da ya sa ake da irin wannan hulda mai kyau tsakanin Sin da Afirka. To, dalili shi ne kasar Sin tana hadin gwiwa da kasashen Afirka bisa wani ra’ayi na tushe, wato akidar gaskiya, da daukar hakikanan matakai, da kauna, da sahihanci, wanda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar. Ban da haka, manufofin kasar Sin da na kasashen Afirka sun nuna cewa, bangarorin 2 suna da ra’ayi iri daya, wato neman ci gaba, da haifar da alfanu ga juna, da kokarin kare adalci a duniya. To, wadannan ra’ayoyi sun sa kasar Sin ke rungumar kasashen Afirka, ko da yake wasu kasashe su kan nuna musu kyama. Ban da haka, a lokacin da kasashen Afirka ke fuskantar takunkumi na harajin kwastam da aka kakaba musu, kasar Sin a nata bangare ta dauki niyyar yafe musu haraji. Kana sabanin yadda wasu kasashe ke tsoma baki cikin harkokin gidan kasashen Afirka, kasar Sin har kullum tana goyon bayan kasashen Afirka a kokarinsu na tabbatar da ikon mulkin kai, gami da kare mutuncinsu.
Jaridar the Vanguard ta kasar Najeriya, ta wallafa wani bayani a kwanan baya, wanda ya ce, al’adar kasar Sin ta tura ministan harkokin wajenta ziyara a kasashen Afirka a farkon duk shekara, ta shaida kauna da girmamawa da kasar take nuna wa bangaren Afirka, wadda ta haifar da hakikanin matakin da ya kusanta kasar Sin da zukatan jama’ar kasashen Afirka. To, muna jiran ganin karin irin wannan mataki da za a dauka a hadin gwiwar Sin da Afirka a shekarar da muke ciki, ta yadda za a rika yaukaka huldar dake tsakaninsu, da tabbatar musu da makoma mai haske, da ta daukacin kasashe masu tasowa. (Bello Wang)















Discussion about this post