ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Huldar Dake Tsakanin Sin Da Afirka Na Kara Yaukaka

by CGTN Hausa and Sulaiman
6 months ago
Sin

Daga ranar Laraba da ta gabata zuwa jiya Litinin, Wang Yi, ministan harkokin wajen kasar Sin ya kai ziyara hedkwatar kungiyar tarayyar Afirka ta AU, da kasashen Habasha, da Tanzania, da Lesotho, daya bayan daya. Ziyararsa ta sake tabbatar da al’adar kasar Sin a fannin diplomasiyya, wato ministan wajen kasar ya kan kai ziyara nahiyar Afirka a farkon duk shekara. Hakika kasar Sin ta riga ta kiyaye wannan al’ada har tsawon shekaru 36.

Minista Wang Yi ya yi tsokaci kan dalilin kasar Sin na kiyaye wannan al’ada, inda ya ce, kasar Sin da kasashen Afirka suna da abokantaka mai zurfi da dogon tarihi, don haka, a ganin kasar Sin, ya kamata ta karfafa wannan hulda da kasashen Afirka a farkon duk shekara, kamar dai yadda wani mutum ke mika gaisuwa da fatan alheri ga ’yan uwansa, gami da ziyartar gidajensu a bikin sabuwar shekara. A zahiri, wannan ziyara da mista Wang Yi ya yi, ta nuna dorewar manufar kasar Sin ta fuskar hulda da kasashen Afirka, da hadin kan kasashe masu tasowa a duniya, gami da aza harsashi ga karin hadin gwiwar bangarorin Sin da Afirka a shekarar da muke ciki.

A yayin ziyararsa a nahiyar Afirka, ministan wajen kasar Sin Wang Yi ya jagoranci taron tattaunawar bangarorin Sin da Afirka kan manyan tsare-tsare, a hadin gwiwarsa da Mahmoud Youssouf, shugaban kwamitin kungiyar AU, inda dukkan bangarorin 2 suka jaddada bukatar karfafa karfi a kokarin kare hakkin Sin da Afirka, da tabbatar da zaman lafiya da ci gaba a duniya. Ban da haka, jami’an 2 sun gane ma idanunsu yadda aka kaddamar da Shekarar Cudanyar Al’ummun Sin Da Afirka, inda a karkashin wannan take, za a gudanar da shirye-shirye kusan 600 da suka shafi harkokin matasa, da ta al’adu, da hadin gwiwar kafofin watsa labaru, da dai sauransu, tsakanin bangarorin Sin da Afirka, a shekarar 2026.

ADVERTISEMENT

Watakila za ka so sanin dalilin da ya sa ake da irin wannan hulda mai kyau tsakanin Sin da Afirka. To, dalili shi ne kasar Sin tana hadin gwiwa da kasashen Afirka bisa wani ra’ayi na tushe, wato akidar gaskiya, da daukar hakikanan matakai, da kauna, da sahihanci, wanda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar. Ban da haka, manufofin kasar Sin da na kasashen Afirka sun nuna cewa, bangarorin 2 suna da ra’ayi iri daya, wato neman ci gaba, da haifar da alfanu ga juna, da kokarin kare adalci a duniya. To, wadannan ra’ayoyi sun sa kasar Sin ke rungumar kasashen Afirka, ko da yake wasu kasashe su kan nuna musu kyama. Ban da haka, a lokacin da kasashen Afirka ke fuskantar takunkumi na harajin kwastam da aka kakaba musu, kasar Sin a nata bangare ta dauki niyyar yafe musu haraji. Kana sabanin yadda wasu kasashe ke tsoma baki cikin harkokin gidan kasashen Afirka, kasar Sin har kullum tana goyon bayan kasashen Afirka a kokarinsu na tabbatar da ikon mulkin kai, gami da kare mutuncinsu.

Jaridar the Vanguard ta kasar Najeriya, ta wallafa wani bayani a kwanan baya, wanda ya ce, al’adar kasar Sin ta tura ministan harkokin wajenta ziyara a kasashen Afirka a farkon duk shekara, ta shaida kauna da girmamawa da kasar take nuna wa bangaren Afirka, wadda ta haifar da hakikanin matakin da ya kusanta kasar Sin da zukatan jama’ar kasashen Afirka. To, muna jiran ganin karin irin wannan mataki da za a dauka a hadin gwiwar Sin da Afirka a shekarar da muke ciki, ta yadda za a rika yaukaka huldar dake tsakaninsu, da tabbatar musu da makoma mai haske, da ta daukacin kasashe masu tasowa. (Bello Wang)

LABARAI MASU NASABA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Next Post
Amurka Ta Miƙa Wa Nijeriya Kayayyakin Soji Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Amurka Ta Miƙa Wa Nijeriya Kayayyakin Soji Domin Yaƙi Da Ta'addanci

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.