ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Huldar Dake Tsakanin Sin Da Afirka Na Kara Yaukaka

by CGTN Hausa and Sulaiman
5 months ago
Sin

Daga ranar Laraba da ta gabata zuwa jiya Litinin, Wang Yi, ministan harkokin wajen kasar Sin ya kai ziyara hedkwatar kungiyar tarayyar Afirka ta AU, da kasashen Habasha, da Tanzania, da Lesotho, daya bayan daya. Ziyararsa ta sake tabbatar da al’adar kasar Sin a fannin diplomasiyya, wato ministan wajen kasar ya kan kai ziyara nahiyar Afirka a farkon duk shekara. Hakika kasar Sin ta riga ta kiyaye wannan al’ada har tsawon shekaru 36.

Minista Wang Yi ya yi tsokaci kan dalilin kasar Sin na kiyaye wannan al’ada, inda ya ce, kasar Sin da kasashen Afirka suna da abokantaka mai zurfi da dogon tarihi, don haka, a ganin kasar Sin, ya kamata ta karfafa wannan hulda da kasashen Afirka a farkon duk shekara, kamar dai yadda wani mutum ke mika gaisuwa da fatan alheri ga ’yan uwansa, gami da ziyartar gidajensu a bikin sabuwar shekara. A zahiri, wannan ziyara da mista Wang Yi ya yi, ta nuna dorewar manufar kasar Sin ta fuskar hulda da kasashen Afirka, da hadin kan kasashe masu tasowa a duniya, gami da aza harsashi ga karin hadin gwiwar bangarorin Sin da Afirka a shekarar da muke ciki.

A yayin ziyararsa a nahiyar Afirka, ministan wajen kasar Sin Wang Yi ya jagoranci taron tattaunawar bangarorin Sin da Afirka kan manyan tsare-tsare, a hadin gwiwarsa da Mahmoud Youssouf, shugaban kwamitin kungiyar AU, inda dukkan bangarorin 2 suka jaddada bukatar karfafa karfi a kokarin kare hakkin Sin da Afirka, da tabbatar da zaman lafiya da ci gaba a duniya. Ban da haka, jami’an 2 sun gane ma idanunsu yadda aka kaddamar da Shekarar Cudanyar Al’ummun Sin Da Afirka, inda a karkashin wannan take, za a gudanar da shirye-shirye kusan 600 da suka shafi harkokin matasa, da ta al’adu, da hadin gwiwar kafofin watsa labaru, da dai sauransu, tsakanin bangarorin Sin da Afirka, a shekarar 2026.

ADVERTISEMENT

Watakila za ka so sanin dalilin da ya sa ake da irin wannan hulda mai kyau tsakanin Sin da Afirka. To, dalili shi ne kasar Sin tana hadin gwiwa da kasashen Afirka bisa wani ra’ayi na tushe, wato akidar gaskiya, da daukar hakikanan matakai, da kauna, da sahihanci, wanda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar. Ban da haka, manufofin kasar Sin da na kasashen Afirka sun nuna cewa, bangarorin 2 suna da ra’ayi iri daya, wato neman ci gaba, da haifar da alfanu ga juna, da kokarin kare adalci a duniya. To, wadannan ra’ayoyi sun sa kasar Sin ke rungumar kasashen Afirka, ko da yake wasu kasashe su kan nuna musu kyama. Ban da haka, a lokacin da kasashen Afirka ke fuskantar takunkumi na harajin kwastam da aka kakaba musu, kasar Sin a nata bangare ta dauki niyyar yafe musu haraji. Kana sabanin yadda wasu kasashe ke tsoma baki cikin harkokin gidan kasashen Afirka, kasar Sin har kullum tana goyon bayan kasashen Afirka a kokarinsu na tabbatar da ikon mulkin kai, gami da kare mutuncinsu.

Jaridar the Vanguard ta kasar Najeriya, ta wallafa wani bayani a kwanan baya, wanda ya ce, al’adar kasar Sin ta tura ministan harkokin wajenta ziyara a kasashen Afirka a farkon duk shekara, ta shaida kauna da girmamawa da kasar take nuna wa bangaren Afirka, wadda ta haifar da hakikanin matakin da ya kusanta kasar Sin da zukatan jama’ar kasashen Afirka. To, muna jiran ganin karin irin wannan mataki da za a dauka a hadin gwiwar Sin da Afirka a shekarar da muke ciki, ta yadda za a rika yaukaka huldar dake tsakaninsu, da tabbatar musu da makoma mai haske, da ta daukacin kasashe masu tasowa. (Bello Wang)

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS
  • Sulaiman
    An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

MASU ALAKA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Next Post
Amurka Ta Miƙa Wa Nijeriya Kayayyakin Soji Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Amurka Ta Miƙa Wa Nijeriya Kayayyakin Soji Domin Yaƙi Da Ta'addanci

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

June 25, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.