ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Huldar Dake Tsakanin Sin Da Afirka Na Kara Yaukaka

by CGTN Hausa and Sulaiman
5 months ago
Sin

Daga ranar Laraba da ta gabata zuwa jiya Litinin, Wang Yi, ministan harkokin wajen kasar Sin ya kai ziyara hedkwatar kungiyar tarayyar Afirka ta AU, da kasashen Habasha, da Tanzania, da Lesotho, daya bayan daya. Ziyararsa ta sake tabbatar da al’adar kasar Sin a fannin diplomasiyya, wato ministan wajen kasar ya kan kai ziyara nahiyar Afirka a farkon duk shekara. Hakika kasar Sin ta riga ta kiyaye wannan al’ada har tsawon shekaru 36.

Minista Wang Yi ya yi tsokaci kan dalilin kasar Sin na kiyaye wannan al’ada, inda ya ce, kasar Sin da kasashen Afirka suna da abokantaka mai zurfi da dogon tarihi, don haka, a ganin kasar Sin, ya kamata ta karfafa wannan hulda da kasashen Afirka a farkon duk shekara, kamar dai yadda wani mutum ke mika gaisuwa da fatan alheri ga ’yan uwansa, gami da ziyartar gidajensu a bikin sabuwar shekara. A zahiri, wannan ziyara da mista Wang Yi ya yi, ta nuna dorewar manufar kasar Sin ta fuskar hulda da kasashen Afirka, da hadin kan kasashe masu tasowa a duniya, gami da aza harsashi ga karin hadin gwiwar bangarorin Sin da Afirka a shekarar da muke ciki.

A yayin ziyararsa a nahiyar Afirka, ministan wajen kasar Sin Wang Yi ya jagoranci taron tattaunawar bangarorin Sin da Afirka kan manyan tsare-tsare, a hadin gwiwarsa da Mahmoud Youssouf, shugaban kwamitin kungiyar AU, inda dukkan bangarorin 2 suka jaddada bukatar karfafa karfi a kokarin kare hakkin Sin da Afirka, da tabbatar da zaman lafiya da ci gaba a duniya. Ban da haka, jami’an 2 sun gane ma idanunsu yadda aka kaddamar da Shekarar Cudanyar Al’ummun Sin Da Afirka, inda a karkashin wannan take, za a gudanar da shirye-shirye kusan 600 da suka shafi harkokin matasa, da ta al’adu, da hadin gwiwar kafofin watsa labaru, da dai sauransu, tsakanin bangarorin Sin da Afirka, a shekarar 2026.

ADVERTISEMENT

Watakila za ka so sanin dalilin da ya sa ake da irin wannan hulda mai kyau tsakanin Sin da Afirka. To, dalili shi ne kasar Sin tana hadin gwiwa da kasashen Afirka bisa wani ra’ayi na tushe, wato akidar gaskiya, da daukar hakikanan matakai, da kauna, da sahihanci, wanda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar. Ban da haka, manufofin kasar Sin da na kasashen Afirka sun nuna cewa, bangarorin 2 suna da ra’ayi iri daya, wato neman ci gaba, da haifar da alfanu ga juna, da kokarin kare adalci a duniya. To, wadannan ra’ayoyi sun sa kasar Sin ke rungumar kasashen Afirka, ko da yake wasu kasashe su kan nuna musu kyama. Ban da haka, a lokacin da kasashen Afirka ke fuskantar takunkumi na harajin kwastam da aka kakaba musu, kasar Sin a nata bangare ta dauki niyyar yafe musu haraji. Kana sabanin yadda wasu kasashe ke tsoma baki cikin harkokin gidan kasashen Afirka, kasar Sin har kullum tana goyon bayan kasashen Afirka a kokarinsu na tabbatar da ikon mulkin kai, gami da kare mutuncinsu.

Jaridar the Vanguard ta kasar Najeriya, ta wallafa wani bayani a kwanan baya, wanda ya ce, al’adar kasar Sin ta tura ministan harkokin wajenta ziyara a kasashen Afirka a farkon duk shekara, ta shaida kauna da girmamawa da kasar take nuna wa bangaren Afirka, wadda ta haifar da hakikanin matakin da ya kusanta kasar Sin da zukatan jama’ar kasashen Afirka. To, muna jiran ganin karin irin wannan mataki da za a dauka a hadin gwiwar Sin da Afirka a shekarar da muke ciki, ta yadda za a rika yaukaka huldar dake tsakaninsu, da tabbatar musu da makoma mai haske, da ta daukacin kasashe masu tasowa. (Bello Wang)

LABARAI MASU NASABA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • Sulaiman
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

MASU ALAKA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki
Ra'ayi Riga

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

June 3, 2026
Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka
Ra'ayi Riga

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

June 1, 2026
Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya

May 29, 2026
Next Post
Amurka Ta Miƙa Wa Nijeriya Kayayyakin Soji Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Amurka Ta Miƙa Wa Nijeriya Kayayyakin Soji Domin Yaƙi Da Ta'addanci

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.