ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, September 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bayelsa: Peter Obi Ya Ziyarci Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Bayelsa 

by Sadiq
4 years ago
Bayelsa

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour Party (LP), Peter Obi, ya ziyarci Yenagoa, babban birnin jihar Bayelsa, inda ya ziyarar wadanda ambaliyar ruwa ta shafa a jihar. 

Obi, wanda ya shiga cikin jihar a cikin wani jirgin saukar ungulu, ya ce abin da ya gani abun tausayi ne kuma babu wata jiha da za ta iya jurewa irin wannan barnar.

  • Juncao, Ciyawar Da Ke Rungumar Makomar Dan Adam Ta Bai Daya
  • Gwamnatin Jigawa Ta Hada Gwiwa Da Kasar Netherland Don Kawo Karshen Ambaliyar Ruwa 

Don haka ya yi kira ga Gwamnatin Tarayya da a gaggauta ayyana dokar ta-baci a kan lamarin ambaliyar a Bayelsa.

ADVERTISEMENT

Obi ya ce, “Na ga illar ambaliya, na je wasu wurare, kuma ban taba ganin irin wannan barnar ba, akwai bukatar gwamnatin tarayya ta sanya dokar ta-baci a Jihar Bayelsa.

“Babu wata jiha da za ta iya tinkarar irin wannan bala’i da kanta, ina kuma kira ga kasashen duniya da kungiyoyin bayar da agaji da su tallafa wa jihohin da abin ya shafa, a Bayelsa muna bukatar taimako, wannan barnar ba za a iya misalta ta ba.”

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ceto Mutane 13 Da ’Yan Bindiga Suka Yi Garkuwa Da Su

Taron BRICS: Shettima Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya Zuwa Indiya

Obi ya ce ya je Yenagoa ne domin jajanta wa gwamnatin jihar da wadanda ambaliyar ruwan ta shafa.

Gwamna Douye Diri wanda ya karbi bakuncin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP a gidan gwamnati da ke Yenagoa kafin ya zarce zuwa sansanin ‘yan gudun hijira da ke tafkin Ox-Bow domin ganewa idanunsa wadanda lamarin ya shafa, ya gode wa Obi bisa nuna goyon baya da ya yi, ya kuma bukaci sauran kungiyoyi da daidaikun jama’a masu kishin kasa da su hada kai da Gwamnatin Jihar wajen bada tallafi ga wadanda ambaliyar ruwa ta shafa.

LEADERSHIP ta rawaito cewar ziyarar da Obi ya kai Bayelsa na zuwa ne kwanaki kadan bayan irin wannan ziyara da ya kai ga wadanda ambaliyar ruwa ta shafa a Jihar Benuwe.

Tun da farko dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP ya sanar da dakatar da yakin neman zabensa saboda iftila’in ambaliyar ruwa wasu sassan kasar.

MASU ALAKA

Labarai

Sojoji Sun Ceto Mutane 13 Da ’Yan Bindiga Suka Yi Garkuwa Da Su

September 11, 2026
Taron BRICS: Shettima Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya Zuwa Indiya
Labarai

Taron BRICS: Shettima Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya Zuwa Indiya

September 11, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
Labarai

Gwamnan Shekara na 2026 Gwamna Caleb Manasseh Mutfwang

September 11, 2026
Next Post
Kasar Sin Ta Yi Kira Da A Yi Cikakken Kokarin Shawo Kan Illar Da Ke Tattare Da Yanayin Da Ake Ciki Game Da Rikicin Rasha Da Ukraine

Kasar Sin Ta Yi Kira Da A Yi Cikakken Kokarin Shawo Kan Illar Da Ke Tattare Da Yanayin Da Ake Ciki Game Da Rikicin Rasha Da Ukraine

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ceto Mutane 13 Da ’Yan Bindiga Suka Yi Garkuwa Da Su

September 11, 2026
Taron BRICS: Shettima Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya Zuwa Indiya

Taron BRICS: Shettima Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya Zuwa Indiya

September 11, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Gwamnan Shekara na 2026 Gwamna Caleb Manasseh Mutfwang

September 11, 2026
Bayelsa

Idan Atiku Ya Janye, Za Mu Kula Da Shi Bayan Mun Yi Nasara – Kwankwaso

September 11, 2026
Bayelsa

ASUU Ta Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki Na Ƙasa Gaba Ɗaya

September 11, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwarzon Gwamnan Shekarar 2026 Kwamared Nasir Idris

September 11, 2026
Bayelsa

Dalilin Da Ya Sa Ba Zan Janye Wa Atiku Ba A Zaɓen 2027 – Peter Obi

September 11, 2026
Farashin Siminti Zai Ragu Idan Farashin Kayan Aiki Ya Sauka – BUA

Gwarzon Shekarar 2026 Abdulsamad Rabiu

September 11, 2026
Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

Buƙatar Ɗaukar Matakan Daƙile Yaɗuwar Cutar Mashaƙo A Nijeriya

September 11, 2026
Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.