ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Juncao, Ciyawar Da Ke Rungumar Makomar Dan Adam Ta Bai Daya

by CMG Hausa
4 years ago
Juncao

Jama’a, ko kun taba jin sunan Juncao? Wannan wata nauin ciyawa ce da ake iya amfani da ita wurin noman laimar kwado da ake iya mai da ita abinci ko magani, wadda ake kiranta ciyawar kasar Sin ko ciyawar samar da arziki a kasashe da dama.

A shekarun 1980, noman laimar kwado ya zama muhimmin aiki da manoma ke dogara a kai wajen saukaka fatara a lardin Fujian da ke kudu maso gabashin kasar Sin. Sai dai hakan ya haifar da matsala a sakamakon yadda manoma suke yawan saran bishiyoyi don yin amfani da su wajen noman laimar kwado.

  • Ya Kamata Amurka Ta Koyi Darasi Daga Yakin Harajin Da Bai Yi Nasara Ba Kan Sin

Ganin haka ya sa Mr. Lin Zhanxi, kwararren masanin ilmin noma da dazuzzuka na kasar Sin, da abokan aikinsa, suka yi kokarin nazari tare da gano fasahar noman laimar kwado ta amfani da nau’in ciyayin Juncao a maimakon katako, a wani kokari na daidaita matsalar.

ADVERTISEMENT

Ta hakan, yawan dazuzzukan da ake sara domin noman laimar kwado ya ragu da yawan gaske. Baya ga haka, sakamakon yadda ciyayin Juncao suka kasance masu iya jure yanayi mai wahala, wadanda kuma suke da saiwoyi masu karfi, baya ga kuma yadda suka kasance masu gina jiki, ya sa bayan noman laimar kwado, ana kuma amfani da su wajen magance iska, da kwararowar hamada, da kuma kiwon dabbobi, wato ke nan, ciyayin na iya taka muhimmiyar rawa wajen raya tattalin arziki da kuma kiyaye muhalli duka.

Daga nan, sai Lin Zhanxi ya yayata fasahar zuwa gundumomi 506 na fadin kasar Sin, fasahar da ta taimaka wajen bude kofar samun arziki ga al’umma da ke fama da talauci a kasar.

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

A bara, akwai wani wasan kwaikwayon talabijin da ya yi matukar samun farin jini a kasar Sin, wanda ya bayyana yadda malami Lin Zhanxi ya yayata fasahar Juncao daga Fujian har zuwa yankin Xihaigu na jihar Ningxia, da ke arewa maso yammacin kasar Sin, ta yadda manoman yankin suka saukaka fatara ta hanyar noman laimar kwado.

Malami Lin Zhanxi bai tsaya a gida ba, a maimakon haka, ya kara yayata fasahar zuwa sauran kasashe da shiyyoyin duniya 106.

A Lesotho, ya kafa tsarin noma da ke iya samar da laimar kwado da nauyinsu ya kai ton 1.2 a kan fadin kasa da bai wuce muraba’in mita 10 kacal ba, matakin da ya zama muhimmiyar kafar samun karin kudi shiga ga manoman wurin.

A kasar Rwanda, kwamitin kula da ayyukan gona na kasar ya yayata fasahar Juncao a sassan kasar wajen kare matsalar lalacewar gonakin kasar. Lallai, ciyayin Juncao sun zama ciyayin samar da arziki da alheri ga al’ummar kasashe masu tasowa da dama.

Daga ranar 16 zuwa 22 ga wata, an gudanar da babban taron wakilan jam’iyyar kwaminis dake kan karagar mulkin kasar Sin karo na 20 a birnin Beijing, kuma Malami Lin Zhanxi ma ya halarci taron a matsayin daya daga cikin wakilai 2296 na jam’iyyar.

A yayin da yake halartar taron, ya kuma kiyaye tuntuba da abokan aikinsa. Wani lokaci, ya kan kuma tashi da tsakan dare, don yin musayar ra’ayoyi tare da takwarorinsa na kasashen Afirka da Latin Amurka.

Rahoton da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar a gun taron na wakilan jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin karo na 20, ya yi nuni da cewa, “Kullum kasar Sin na nacewa ga bin manufar diplomasiyya, ta kiyaye zaman lafiyar duniya da tabbatar da samun ci gaban juna, don rungumar makomar dan Adam ta bai daya.” “kasar Sin za ta karfafa hadin gwiwa da kasashe masu tasowa bisa sahihanci da gaskiya, don kiyaye moriyarsu ta bai daya”.

A game da wannan, malami Lin Zhanxi ya bayyana cewa, “Kasar Sin na samar da gudummawar fasahohinta a fannin ayyukan gona ba tare da gindaya wani sharadi ba, kuma muna samar da sahihiyar gudummawarmu, don fatan ganin an saukaka fatara.”

A shekarar 2020, kasar Sin ta cimma nasarar fitar da al’umma kusan miliyan 100 a karkarar kasar Sin daga kangin talauci, kuma kasancewarta kasa mai tasowa mafi girma a duniya, ba ta manta da sauran kasashe masu tasowa ba, har ma ta raba musu fasahohinta ba tare da boye komai ba, don rungumar makomar dan Adam ta bai daya. (Mai Zane: Mustapha Bulama)

Juncao
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
Daga Birnin Sin

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
Daga Birnin Sin

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
Daga Birnin Sin

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Next Post
Bayelsa: Peter Obi Ya Ziyarci Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Bayelsa 

Bayelsa: Peter Obi Ya Ziyarci Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Bayelsa 

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.