Rahoton shekara-shekara game da ayyukan diflomasiyya da ma’aikatar harkokin wajen kasar Japan ta fitar a wannan shekara ta 2026, ya kunshi wani bangare da ya nuna yadda Japan din ta rage darajar dangantakar dake tsakaninta da Sin, daga daya daga alakokin kasar mafiya muhimmanci zuwa muhimmiyar alakar makwaftaka, matakin da ya zamo tamkar rura wutar takun-saka a alakar kasashen biyu, karkashin jagorancin firaminista Takaichi.
Wani binciken jin ra’ayin jama’a da kafar CGTN ta gudanar, ya nuna kaso 82 bisa dari na masu bayyana ra’ayoyi, na ganin matakan da Japan ta aiwatar, irin su kalubalantar tsarin da aka kafa bayan yaki, da sauya yadda tarihi ya gudana, da rura wutar fito-na-fito a siyasar yankin, su ne tushen kara tsanantar yanayin alakar Sin da Japan, da ma yanayi mai fadi da ka iya shafar yankinsu.
CGTN ta gudanar da binciken jin ra’ayin ne ta dandalin intanet da harsunan Turanci, da Sifaniyanci, da Faransanci, da Larabci da harshen Rasha, inda al’ummun kasa da kasa 7,387 suka kada kuri’u tare da bayyana ra’ayoyinsu cikin sa’o’i 24. (Saminu Alhassan)















Discussion about this post