ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 6, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwankwasiyya Ta Kai Ƙorafi DSS Kan Zargin Cin Zarafin Kwankwaso A Shafukan Sada Zumunta

by Muhammad
3 months ago
Screenshot

Screenshot

Ƙungiyar Kwankwasiyya ta kai ƙorafi Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS) a Jihar Kano, inda ta zargi wasu jami’an Gwamnatin Kano da cin zarafin Kwankwaso ta shafukan sada zumunta, da musgunawa da kuma ɓata suna da ake yi wa shugabanninta a kafafen sada zumunta.

A cikin ƙorafin da aka rubuta ranar 9 ga Afrilu, 2026, aka aika wa Daraktan DSS na Jihar Kano, ƙungiyar ta buƙaci a gaggauta gudanar da bincike kan abin da ta bayyana a matsayin cin zarafi da ɓata sunan manyan mambobinta.

  • Yanzu- Yanzu Atiku, Obi, Kwankwaso, Mark Da Sauransu Sun Jagoranci Zanga-Zanga Zuwa INEC
  • 2027: Obi Da Kwankwaso Za Su Fafata Da Atiku Wajen Neman Takarar Shugaban Kasa A ADC

Waɗanda abin ya shafa sun haɗa da Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, Kwamared Aminu Abdussalam Gwarzo, Sanata Rufa’i Sani Hanga, da sauran jiga-jigan ƙungiyar Kwankwasiyya.

ADVERTISEMENT

Ƙorafin ya kuma yi zargin cewa wasu mutane da ke riƙe da muƙaman siyasa da na yaɗa labarai a gwamnatin Jihar Kano na da hannu a wannan shiri na cin zarafi ta intanet.

Daga cikin waɗanda aka ambata akwai Sanusi Bature Dawakin Tofa, mai magana da yawun gwamnan jihar; Salisu Yahaya Hotoro, shugaban matasan APC; Ibrahim Adam, mai bai wa gwamna shawara kan harkokin yaɗa labarai; Nuhu Dambazau, babban mai bayar da rahoto na musamman ga gwamna; da kuma Mukhtar S. Yahuza, da sauransu.

LABARAI MASU NASABA

Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija

Atiku Ya Naɗa Kenneth Okonkwo A Matsayin Kakakin Yaƙin Neman Zaɓensa

A cewar masu ƙorafin, ana zargin waɗannan mutane da amfani da shafukansu na sada zumunta daban-daban, musamman Facebook, wajen yaɗa “saƙonni na ɓata suna” kan shugabanni da magoya bayan ƙungiyar.

Ƙungiyar ta ce:

“Mun rubuto domin gabatar da ƙorafi a hukumance ga ofishinku dangane da ci gaba da cin zarafi ta yanar gizo, musgunawa, da kuma ɓata suna da ake yi wa shugabannin ƙungiyar Kwankwasiyya.”

Ta kuma buƙaci DSS da ta gudanar da cikakken bincike kan waɗannan zarge-zarge tare da ɗaukar matakan da suka dace, tana mai cewa lamarin na zama barazana ga zaman lafiyar siyasa da kuma mu’amala cikin lumana a kafafen sadarwar zamani a jihar.

Kwankwasiyya
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija
Siyasa

Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija

July 5, 2026
Atiku
Siyasa

Atiku Ya Naɗa Kenneth Okonkwo A Matsayin Kakakin Yaƙin Neman Zaɓensa

July 2, 2026
‘Yan Adawa Sun Mayar Da Matsalar Tsaro Siyasa – Yusuf Gagdi
Manyan Labarai

‘Yan Adawa Sun Mayar Da Matsalar Tsaro Siyasa – Yusuf Gagdi

July 1, 2026
Next Post
Shugabar Jam’iyyar Kuomintang Ta Kai Ziyarar Girmamawa Kabarin Tunawa Da Sun Yat-sen Dake Birnin Beijing

Shugabar Jam’iyyar Kuomintang Ta Kai Ziyarar Girmamawa Kabarin Tunawa Da Sun Yat-sen Dake Birnin Beijing

LABARAI MASU NASABA

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

July 5, 2026
Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

July 5, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

July 5, 2026
An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

July 5, 2026
Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

July 5, 2026
Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

July 5, 2026
Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

July 5, 2026
Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

July 5, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

July 5, 2026
Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

July 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.