ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwankwasiyya Ta Kai Ƙorafi DSS Kan Zargin Cin Zarafin Kwankwaso A Shafukan Sada Zumunta

by Muhammad
4 months ago
Screenshot

Screenshot

Ƙungiyar Kwankwasiyya ta kai ƙorafi Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS) a Jihar Kano, inda ta zargi wasu jami’an Gwamnatin Kano da cin zarafin Kwankwaso ta shafukan sada zumunta, da musgunawa da kuma ɓata suna da ake yi wa shugabanninta a kafafen sada zumunta.

A cikin ƙorafin da aka rubuta ranar 9 ga Afrilu, 2026, aka aika wa Daraktan DSS na Jihar Kano, ƙungiyar ta buƙaci a gaggauta gudanar da bincike kan abin da ta bayyana a matsayin cin zarafi da ɓata sunan manyan mambobinta.

  • Yanzu- Yanzu Atiku, Obi, Kwankwaso, Mark Da Sauransu Sun Jagoranci Zanga-Zanga Zuwa INEC
  • 2027: Obi Da Kwankwaso Za Su Fafata Da Atiku Wajen Neman Takarar Shugaban Kasa A ADC

Waɗanda abin ya shafa sun haɗa da Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, Kwamared Aminu Abdussalam Gwarzo, Sanata Rufa’i Sani Hanga, da sauran jiga-jigan ƙungiyar Kwankwasiyya.

ADVERTISEMENT

Ƙorafin ya kuma yi zargin cewa wasu mutane da ke riƙe da muƙaman siyasa da na yaɗa labarai a gwamnatin Jihar Kano na da hannu a wannan shiri na cin zarafi ta intanet.

Daga cikin waɗanda aka ambata akwai Sanusi Bature Dawakin Tofa, mai magana da yawun gwamnan jihar; Salisu Yahaya Hotoro, shugaban matasan APC; Ibrahim Adam, mai bai wa gwamna shawara kan harkokin yaɗa labarai; Nuhu Dambazau, babban mai bayar da rahoto na musamman ga gwamna; da kuma Mukhtar S. Yahuza, da sauransu.

LABARAI MASU NASABA

2027: Magoya Bayan Tinubu Sun Yi Watsi Da Sukar Takarar Musulmi-Musulmi Da Kwankwaso Ya Yi

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

A cewar masu ƙorafin, ana zargin waɗannan mutane da amfani da shafukansu na sada zumunta daban-daban, musamman Facebook, wajen yaɗa “saƙonni na ɓata suna” kan shugabanni da magoya bayan ƙungiyar.

Ƙungiyar ta ce:

“Mun rubuto domin gabatar da ƙorafi a hukumance ga ofishinku dangane da ci gaba da cin zarafi ta yanar gizo, musgunawa, da kuma ɓata suna da ake yi wa shugabannin ƙungiyar Kwankwasiyya.”

Ta kuma buƙaci DSS da ta gudanar da cikakken bincike kan waɗannan zarge-zarge tare da ɗaukar matakan da suka dace, tana mai cewa lamarin na zama barazana ga zaman lafiyar siyasa da kuma mu’amala cikin lumana a kafafen sadarwar zamani a jihar.

Kwankwasiyya
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100
  • Muhammad
    ‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye

MASU ALAKA

Kwankwaso Zai Koma ADC Ranar Litinin
Manyan Labarai

2027: Magoya Bayan Tinubu Sun Yi Watsi Da Sukar Takarar Musulmi-Musulmi Da Kwankwaso Ya Yi

July 22, 2026
Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC
Labarai

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

July 21, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Next Post
Shugabar Jam’iyyar Kuomintang Ta Kai Ziyarar Girmamawa Kabarin Tunawa Da Sun Yat-sen Dake Birnin Beijing

Shugabar Jam’iyyar Kuomintang Ta Kai Ziyarar Girmamawa Kabarin Tunawa Da Sun Yat-sen Dake Birnin Beijing

LABARAI MASU NASABA

Kwankwasiyya

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

July 26, 2026
Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

July 26, 2026
Kwankwasiyya

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

July 26, 2026
Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

July 26, 2026
Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

July 26, 2026
Kwankwasiyya

Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi

July 26, 2026
Bala Mohammed

Sadakin Budurwa ₦3,000 Na Bazawara ₦1,500: Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaryata Batun

July 26, 2026
Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

July 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.