Ƙungiyar Kwankwasiyya ta kai ƙorafi Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS) a Jihar Kano, inda ta zargi wasu jami’an Gwamnatin Kano da cin zarafin Kwankwaso ta shafukan sada zumunta, da musgunawa da kuma ɓata suna da ake yi wa shugabanninta a kafafen sada zumunta.
A cikin ƙorafin da aka rubuta ranar 9 ga Afrilu, 2026, aka aika wa Daraktan DSS na Jihar Kano, ƙungiyar ta buƙaci a gaggauta gudanar da bincike kan abin da ta bayyana a matsayin cin zarafi da ɓata sunan manyan mambobinta.
- Yanzu- Yanzu Atiku, Obi, Kwankwaso, Mark Da Sauransu Sun Jagoranci Zanga-Zanga Zuwa INEC
- 2027: Obi Da Kwankwaso Za Su Fafata Da Atiku Wajen Neman Takarar Shugaban Kasa A ADC
Waɗanda abin ya shafa sun haɗa da Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, Kwamared Aminu Abdussalam Gwarzo, Sanata Rufa’i Sani Hanga, da sauran jiga-jigan ƙungiyar Kwankwasiyya.
Ƙorafin ya kuma yi zargin cewa wasu mutane da ke riƙe da muƙaman siyasa da na yaɗa labarai a gwamnatin Jihar Kano na da hannu a wannan shiri na cin zarafi ta intanet.
Daga cikin waɗanda aka ambata akwai Sanusi Bature Dawakin Tofa, mai magana da yawun gwamnan jihar; Salisu Yahaya Hotoro, shugaban matasan APC; Ibrahim Adam, mai bai wa gwamna shawara kan harkokin yaɗa labarai; Nuhu Dambazau, babban mai bayar da rahoto na musamman ga gwamna; da kuma Mukhtar S. Yahuza, da sauransu.
A cewar masu ƙorafin, ana zargin waɗannan mutane da amfani da shafukansu na sada zumunta daban-daban, musamman Facebook, wajen yaɗa “saƙonni na ɓata suna” kan shugabanni da magoya bayan ƙungiyar.
Ƙungiyar ta ce:
“Mun rubuto domin gabatar da ƙorafi a hukumance ga ofishinku dangane da ci gaba da cin zarafi ta yanar gizo, musgunawa, da kuma ɓata suna da ake yi wa shugabannin ƙungiyar Kwankwasiyya.”
Ta kuma buƙaci DSS da ta gudanar da cikakken bincike kan waɗannan zarge-zarge tare da ɗaukar matakan da suka dace, tana mai cewa lamarin na zama barazana ga zaman lafiyar siyasa da kuma mu’amala cikin lumana a kafafen sadarwar zamani a jihar.















Discussion about this post