ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ci Gaban Al’umma: Amina Muhammad Ta Jinjina Wa Gwamnan Zamfara

by Sulaiman
2 months ago
Zamfara

Mataimakiyar Babban Sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD), Amina Mohammed, ta bayyana cewa Jihar Zamfara yanzu ta zama mai sauƙin isa ga masu zuba jari da abokan hulɗa, tare da jaddada cewa majalisar na shirye ta zama abokiyar hulɗa wajen bunƙasa jihar.

 

Amina Mohammed ta yi wannan bayani ne yayin wata ziyarar aiki da ta kai jihar Zamfara a ranar Alhamis, inda ta jagoranci tawagar manyan jami’an MDD domin duba halin da ake ciki a fannoni daban-daban.

ADVERTISEMENT
  • Ƙarin Farashin Man Fetur: TUC Ta Shawarci Gwamnati Ta Tallafawa Matatun Mai Na Cikin Gida
  • NDLEA Ta Bankaɗo Hodar Ibilis Da Aka Ɓoye A Cikin Gwangwanin Kwakwar Manja A Legas

Sanarwar da mai magana da yawun gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta ce Mataimakiyar Babban Sakataren ta kai ziyarar gani da ido a Ƙaramar Hukumar Maru da wasu muhimman wurare, domin tantance ayyukan ci gaba da kuma fahimtar buƙatun al’umma kai tsaye.

 

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Tawagar ta haɗa da wakilan manyan hukumomin MDD, ciki har da wakilin Shirin Raya Ƙasa na Majalisar Ɗinkin Duniya a Nijeriya, Elsie Attafuah; da shugabannin ƙasa na hukumomi irin su UNICEF, Hukumar Kula da Hijira ta Duniya, UNHCR, UNODC, UNAIDS da UNFPA.

 

A yayin gabatar da bayanai na bangarori daban-daban, Gwamna Dauda Lawal ya bayyana cewa gwamnatinsa na da tsare-tsare masu ƙarfi domin inganta ci gaba mai ɗorewa, da jure sauyin yanayi, da kuma haɓaka tattalin arziki mai haɗa kowa da kowa ta hanyar haɗin gwiwa.

 

Ya ƙara da cewa, Zamfara na kan wani muhimmin mataki na kawo sauyi, inda yawancin al’ummar jihar ke dogaro da noma, wanda ke zama ginshiƙin tattalin arzikinta.

 

A cewarsa, tsarin “Ajandar Ceto mai maki shida” wata dabara ce da aka tsara domin farfaɗo da jihar tare da tabbatar da ci gaba mai ɗorewa.

 

A nata jawabin, Amina Mohammed ta yaba da yadda gwamnatin Zamfara ta gabatar da tsare-tsarenta cikin tsari, tana mai cewa hakan ya isa ya ja hankalin masu zuba jari da abokan hulɗa.

 

Ta ce, “Masu zuba jari na buƙatar yanayi mai kyau. Abin da ake buƙata yanzu shi ne zaman lafiya domin jawo hankalinsu. Abin da muka gani a yau ya nuna ƙwazon shugabanci da kuma hangen nesa, wanda shi ne abin da masu zuba jari ke nema.”

 

Ta kuma jaddada cewa, Zamfara na da ɗimbin damar ci gaba musamman a fannin ma’adinai, kasuwanci da noma, tare da nuna cewa akwai buƙatar haɗin kai daga kowane ɓangare domin cimma nasara.

 

“Na ga dama mai yawa, na ga kasuwa da buƙata, sannan na ga shugabanci da ke shirye ya haɗa kai da cibiyoyi da abokan hulɗa domin cimma nasara. Wannan aiki ba na gwamna kaɗai ba ne — kowa na da rawar da zai taka,” inji ta.

 

A ƙarshe, ta bayyana cewa MDD za ta ci gaba da tallafa wa jihar Zamfara, tana mai cewa, “Akwai fata mai yawa a nan, kuma muna shirye mu zama sahihin abokan hulɗa domin ganin an cimma burin ci gaba mai ɗorewa.”

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
Jimillar Darajar Kayayyakin Da Ake Samarwa a Cibiyoyin Fasaha Na Kasar Sin a 2025 Ta Zarce Yuan Tiriliyan 20

Jimillar Darajar Kayayyakin Da Ake Samarwa a Cibiyoyin Fasaha Na Kasar Sin a 2025 Ta Zarce Yuan Tiriliyan 20

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.