ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ci Gaban Al’umma: Amina Muhammad Ta Jinjina Wa Gwamnan Zamfara

by Sulaiman
3 months ago
Zamfara

Mataimakiyar Babban Sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD), Amina Mohammed, ta bayyana cewa Jihar Zamfara yanzu ta zama mai sauƙin isa ga masu zuba jari da abokan hulɗa, tare da jaddada cewa majalisar na shirye ta zama abokiyar hulɗa wajen bunƙasa jihar.

 

Amina Mohammed ta yi wannan bayani ne yayin wata ziyarar aiki da ta kai jihar Zamfara a ranar Alhamis, inda ta jagoranci tawagar manyan jami’an MDD domin duba halin da ake ciki a fannoni daban-daban.

ADVERTISEMENT
  • Ƙarin Farashin Man Fetur: TUC Ta Shawarci Gwamnati Ta Tallafawa Matatun Mai Na Cikin Gida
  • NDLEA Ta Bankaɗo Hodar Ibilis Da Aka Ɓoye A Cikin Gwangwanin Kwakwar Manja A Legas

Sanarwar da mai magana da yawun gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta ce Mataimakiyar Babban Sakataren ta kai ziyarar gani da ido a Ƙaramar Hukumar Maru da wasu muhimman wurare, domin tantance ayyukan ci gaba da kuma fahimtar buƙatun al’umma kai tsaye.

 

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Tawagar ta haɗa da wakilan manyan hukumomin MDD, ciki har da wakilin Shirin Raya Ƙasa na Majalisar Ɗinkin Duniya a Nijeriya, Elsie Attafuah; da shugabannin ƙasa na hukumomi irin su UNICEF, Hukumar Kula da Hijira ta Duniya, UNHCR, UNODC, UNAIDS da UNFPA.

 

A yayin gabatar da bayanai na bangarori daban-daban, Gwamna Dauda Lawal ya bayyana cewa gwamnatinsa na da tsare-tsare masu ƙarfi domin inganta ci gaba mai ɗorewa, da jure sauyin yanayi, da kuma haɓaka tattalin arziki mai haɗa kowa da kowa ta hanyar haɗin gwiwa.

 

Ya ƙara da cewa, Zamfara na kan wani muhimmin mataki na kawo sauyi, inda yawancin al’ummar jihar ke dogaro da noma, wanda ke zama ginshiƙin tattalin arzikinta.

 

A cewarsa, tsarin “Ajandar Ceto mai maki shida” wata dabara ce da aka tsara domin farfaɗo da jihar tare da tabbatar da ci gaba mai ɗorewa.

 

A nata jawabin, Amina Mohammed ta yaba da yadda gwamnatin Zamfara ta gabatar da tsare-tsarenta cikin tsari, tana mai cewa hakan ya isa ya ja hankalin masu zuba jari da abokan hulɗa.

 

Ta ce, “Masu zuba jari na buƙatar yanayi mai kyau. Abin da ake buƙata yanzu shi ne zaman lafiya domin jawo hankalinsu. Abin da muka gani a yau ya nuna ƙwazon shugabanci da kuma hangen nesa, wanda shi ne abin da masu zuba jari ke nema.”

 

Ta kuma jaddada cewa, Zamfara na da ɗimbin damar ci gaba musamman a fannin ma’adinai, kasuwanci da noma, tare da nuna cewa akwai buƙatar haɗin kai daga kowane ɓangare domin cimma nasara.

 

“Na ga dama mai yawa, na ga kasuwa da buƙata, sannan na ga shugabanci da ke shirye ya haɗa kai da cibiyoyi da abokan hulɗa domin cimma nasara. Wannan aiki ba na gwamna kaɗai ba ne — kowa na da rawar da zai taka,” inji ta.

 

A ƙarshe, ta bayyana cewa MDD za ta ci gaba da tallafa wa jihar Zamfara, tana mai cewa, “Akwai fata mai yawa a nan, kuma muna shirye mu zama sahihin abokan hulɗa domin ganin an cimma burin ci gaba mai ɗorewa.”

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Jimillar Darajar Kayayyakin Da Ake Samarwa a Cibiyoyin Fasaha Na Kasar Sin a 2025 Ta Zarce Yuan Tiriliyan 20

Jimillar Darajar Kayayyakin Da Ake Samarwa a Cibiyoyin Fasaha Na Kasar Sin a 2025 Ta Zarce Yuan Tiriliyan 20

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.