ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ci Gaban Al’umma: Amina Muhammad Ta Jinjina Wa Gwamnan Zamfara

by Sulaiman
3 months ago
Zamfara

Mataimakiyar Babban Sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD), Amina Mohammed, ta bayyana cewa Jihar Zamfara yanzu ta zama mai sauƙin isa ga masu zuba jari da abokan hulɗa, tare da jaddada cewa majalisar na shirye ta zama abokiyar hulɗa wajen bunƙasa jihar.

 

Amina Mohammed ta yi wannan bayani ne yayin wata ziyarar aiki da ta kai jihar Zamfara a ranar Alhamis, inda ta jagoranci tawagar manyan jami’an MDD domin duba halin da ake ciki a fannoni daban-daban.

ADVERTISEMENT
  • Ƙarin Farashin Man Fetur: TUC Ta Shawarci Gwamnati Ta Tallafawa Matatun Mai Na Cikin Gida
  • NDLEA Ta Bankaɗo Hodar Ibilis Da Aka Ɓoye A Cikin Gwangwanin Kwakwar Manja A Legas

Sanarwar da mai magana da yawun gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta ce Mataimakiyar Babban Sakataren ta kai ziyarar gani da ido a Ƙaramar Hukumar Maru da wasu muhimman wurare, domin tantance ayyukan ci gaba da kuma fahimtar buƙatun al’umma kai tsaye.

 

LABARAI MASU NASABA

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Tawagar ta haɗa da wakilan manyan hukumomin MDD, ciki har da wakilin Shirin Raya Ƙasa na Majalisar Ɗinkin Duniya a Nijeriya, Elsie Attafuah; da shugabannin ƙasa na hukumomi irin su UNICEF, Hukumar Kula da Hijira ta Duniya, UNHCR, UNODC, UNAIDS da UNFPA.

 

A yayin gabatar da bayanai na bangarori daban-daban, Gwamna Dauda Lawal ya bayyana cewa gwamnatinsa na da tsare-tsare masu ƙarfi domin inganta ci gaba mai ɗorewa, da jure sauyin yanayi, da kuma haɓaka tattalin arziki mai haɗa kowa da kowa ta hanyar haɗin gwiwa.

 

Ya ƙara da cewa, Zamfara na kan wani muhimmin mataki na kawo sauyi, inda yawancin al’ummar jihar ke dogaro da noma, wanda ke zama ginshiƙin tattalin arzikinta.

 

A cewarsa, tsarin “Ajandar Ceto mai maki shida” wata dabara ce da aka tsara domin farfaɗo da jihar tare da tabbatar da ci gaba mai ɗorewa.

 

A nata jawabin, Amina Mohammed ta yaba da yadda gwamnatin Zamfara ta gabatar da tsare-tsarenta cikin tsari, tana mai cewa hakan ya isa ya ja hankalin masu zuba jari da abokan hulɗa.

 

Ta ce, “Masu zuba jari na buƙatar yanayi mai kyau. Abin da ake buƙata yanzu shi ne zaman lafiya domin jawo hankalinsu. Abin da muka gani a yau ya nuna ƙwazon shugabanci da kuma hangen nesa, wanda shi ne abin da masu zuba jari ke nema.”

 

Ta kuma jaddada cewa, Zamfara na da ɗimbin damar ci gaba musamman a fannin ma’adinai, kasuwanci da noma, tare da nuna cewa akwai buƙatar haɗin kai daga kowane ɓangare domin cimma nasara.

 

“Na ga dama mai yawa, na ga kasuwa da buƙata, sannan na ga shugabanci da ke shirye ya haɗa kai da cibiyoyi da abokan hulɗa domin cimma nasara. Wannan aiki ba na gwamna kaɗai ba ne — kowa na da rawar da zai taka,” inji ta.

 

A ƙarshe, ta bayyana cewa MDD za ta ci gaba da tallafa wa jihar Zamfara, tana mai cewa, “Akwai fata mai yawa a nan, kuma muna shirye mu zama sahihin abokan hulɗa domin ganin an cimma burin ci gaba mai ɗorewa.”

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman
  • Sulaiman
    Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI
Ra'ayi Riga

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya
Labarai

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
Next Post
Jimillar Darajar Kayayyakin Da Ake Samarwa a Cibiyoyin Fasaha Na Kasar Sin a 2025 Ta Zarce Yuan Tiriliyan 20

Jimillar Darajar Kayayyakin Da Ake Samarwa a Cibiyoyin Fasaha Na Kasar Sin a 2025 Ta Zarce Yuan Tiriliyan 20

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.