ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ci Gaban Al’umma: Amina Muhammad Ta Jinjina Wa Gwamnan Zamfara

by Sulaiman
5 months ago
Zamfara

Mataimakiyar Babban Sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD), Amina Mohammed, ta bayyana cewa Jihar Zamfara yanzu ta zama mai sauƙin isa ga masu zuba jari da abokan hulɗa, tare da jaddada cewa majalisar na shirye ta zama abokiyar hulɗa wajen bunƙasa jihar.

 

Amina Mohammed ta yi wannan bayani ne yayin wata ziyarar aiki da ta kai jihar Zamfara a ranar Alhamis, inda ta jagoranci tawagar manyan jami’an MDD domin duba halin da ake ciki a fannoni daban-daban.

ADVERTISEMENT
  • Ƙarin Farashin Man Fetur: TUC Ta Shawarci Gwamnati Ta Tallafawa Matatun Mai Na Cikin Gida
  • NDLEA Ta Bankaɗo Hodar Ibilis Da Aka Ɓoye A Cikin Gwangwanin Kwakwar Manja A Legas

Sanarwar da mai magana da yawun gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta ce Mataimakiyar Babban Sakataren ta kai ziyarar gani da ido a Ƙaramar Hukumar Maru da wasu muhimman wurare, domin tantance ayyukan ci gaba da kuma fahimtar buƙatun al’umma kai tsaye.

 

LABARAI MASU NASABA

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Tawagar ta haɗa da wakilan manyan hukumomin MDD, ciki har da wakilin Shirin Raya Ƙasa na Majalisar Ɗinkin Duniya a Nijeriya, Elsie Attafuah; da shugabannin ƙasa na hukumomi irin su UNICEF, Hukumar Kula da Hijira ta Duniya, UNHCR, UNODC, UNAIDS da UNFPA.

 

A yayin gabatar da bayanai na bangarori daban-daban, Gwamna Dauda Lawal ya bayyana cewa gwamnatinsa na da tsare-tsare masu ƙarfi domin inganta ci gaba mai ɗorewa, da jure sauyin yanayi, da kuma haɓaka tattalin arziki mai haɗa kowa da kowa ta hanyar haɗin gwiwa.

 

Ya ƙara da cewa, Zamfara na kan wani muhimmin mataki na kawo sauyi, inda yawancin al’ummar jihar ke dogaro da noma, wanda ke zama ginshiƙin tattalin arzikinta.

 

A cewarsa, tsarin “Ajandar Ceto mai maki shida” wata dabara ce da aka tsara domin farfaɗo da jihar tare da tabbatar da ci gaba mai ɗorewa.

 

A nata jawabin, Amina Mohammed ta yaba da yadda gwamnatin Zamfara ta gabatar da tsare-tsarenta cikin tsari, tana mai cewa hakan ya isa ya ja hankalin masu zuba jari da abokan hulɗa.

 

Ta ce, “Masu zuba jari na buƙatar yanayi mai kyau. Abin da ake buƙata yanzu shi ne zaman lafiya domin jawo hankalinsu. Abin da muka gani a yau ya nuna ƙwazon shugabanci da kuma hangen nesa, wanda shi ne abin da masu zuba jari ke nema.”

 

Ta kuma jaddada cewa, Zamfara na da ɗimbin damar ci gaba musamman a fannin ma’adinai, kasuwanci da noma, tare da nuna cewa akwai buƙatar haɗin kai daga kowane ɓangare domin cimma nasara.

 

“Na ga dama mai yawa, na ga kasuwa da buƙata, sannan na ga shugabanci da ke shirye ya haɗa kai da cibiyoyi da abokan hulɗa domin cimma nasara. Wannan aiki ba na gwamna kaɗai ba ne — kowa na da rawar da zai taka,” inji ta.

 

A ƙarshe, ta bayyana cewa MDD za ta ci gaba da tallafa wa jihar Zamfara, tana mai cewa, “Akwai fata mai yawa a nan, kuma muna shirye mu zama sahihin abokan hulɗa domin ganin an cimma burin ci gaba mai ɗorewa.”

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
  • Sulaiman
    Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
  • Sulaiman
    Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
  • Sulaiman
    Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

MASU ALAKA

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara
Labarai

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia
Manyan Labarai

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya
Labarai

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
Next Post
Jimillar Darajar Kayayyakin Da Ake Samarwa a Cibiyoyin Fasaha Na Kasar Sin a 2025 Ta Zarce Yuan Tiriliyan 20

Jimillar Darajar Kayayyakin Da Ake Samarwa a Cibiyoyin Fasaha Na Kasar Sin a 2025 Ta Zarce Yuan Tiriliyan 20

LABARAI MASU NASABA

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.