ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NDLEA Ta Bankaɗo Hodar Ibilis Da Aka Ɓoye A Cikin Gwangwanin Kwakwar Manja A Legas

by Yusuf Shuaibu
2 months ago
NDLEA

Jami’an Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Ƙasa (NDLEA) sun yi nasarar tarwatsa wata babbar ƙungiyar safarar miyagun ƙwayoyi bayan wani shiri na sirri da ya ɗauki tsawon makonni uku.

A yayin wannan aiki, an daƙile jigilar hodar ibilis da aka ɓoye cikin gwangwanin man ƙwarya da ake shirin tura wa zuwa ƙasar Birtaniya, tare da kai samame wurin da ake shirya kayan, lamarin da ya kai ga gano dukkan matakan ƙungiyar har zuwa kama jagoranta.

  • Kwastam Ta Kama Miyagun Ƙwayoyi Na Naira Miliyan 99.9, Ta Miƙa Su Ga NDLEA A Sakkwato
  • NDLEA Ta Kwace Kwayoyin Pregabalin 75,000 Da Hodar Iblis 556 A Kano

Nasaran ta fara ne tun a ranar da jami’an NDLEA da ke Ikeja a Jihar Legas suka gano kilo 3.10 na hodar ibilis a sashen fitar da kaya na filin jirgin sama. An ɓoye ƙwayar cikin gwangwanin kwakwar manja da aka shirya tura wa Birtaniya.

ADVERTISEMENT

Nan take aka kama masu kula da kayan guda biyu da suka haɗa da Idris Olayiwola Amoo da Akinlami Akinsoji Adedoyin. Domin gano wanda ya aika da kayan da kuma jagoran ƙungiyar, jami’an suka gudanar da wani aiki na musamman ranar Alhamis 2 ga Afrilu wanda ya kai ga kama Ezemuwo Joel, wanda ke amfani da sunan ƙarya na Ajayi.

Kamen nasa ya kai jami’an ga jagoran ƙungiyar, King Arinze mai shekaru 52, wanda aka cafke a maboyarsa a yankin Isolo a Legas. Daga nan aka kai shi rumbun ajiyarsa da ke 11, Ola Ifa Street, Bucknor, Isolo, inda aka gano gwangwani 886 na kwakwar manja da aka shirya don ɓoye miyagun ƙwayoyi, da kayan aiki irinsu na’urar rufe gwangwani, masu buɗe gwangwani, fenti, gram 52 na cannabis satiɓa da safar hannu. Ya amsa cewa shi ne ke zubar da man daga gwangwanin domin ɓoye hodar ibilis.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

A wani aiki daban a Jihar Borno, jami’an NDLEA a ranar Laraba 1 ga Afrilu sun kama wata mata mai bai wa ƙungiyoyin ƴan bindiga miyagun ƙwayoyi, Aisha Adamu mai shekaru 28, a kan titin Gamboru Ngala, ɗauke da kilo 4.3 na Colorado, wani nau’in tabar wiwi ta roba mai ƙarfi.

A gefe guda kuma, jami’an NDLEA sun kama faston cocin Celestial Church of Christ da ke Agonɓi Sea Beach, yankin Sakpo a Seme, Badagry, Fasto Afolabi Hodonu mai shekaru 45, tare da matarsa, Mrs. Success Hodonu mai shekaru 35, ranar Alhamis 2 ga Afrilu a shingen bincike na Gbaji. Binciken motarsu ƙirar Honda Pilot ya kai ga gano kilo 11 na skunk da aka ɓoye a sassan motar.

Kamen ma’auratan ya biyo bayan cafke wani da ya yi ƙaryar zama jami’in tsaro, Sunday Samuel mai shekaru 35, a wannan shingen ranar Litinin 30 ga Maris, ɗauke da kilo 24.5 na skunk daga Seme zuwa Legas.

A Jihar Adamawa, jami’an NDLEA da ke sintiri a kan titin Namtari, Yola ta kudu, ranar Litinin 30 ga Maris sun tare wata mota mai lamba RUW 947 ƊA ɗauke da ƙwayoyi 48,000 na tramadol. An kama direban, Abdulaziz Ismail Korede, yayin da bincike ya kai ga kama mai karɓar kayan, Idris Adamu.

A Jihar Osun, an kama Idiatu Oladejo mai shekaru 60 da kilo 15 na skunk a Isale Osun, Osogbo, ranar Laraba 1 ga Afrilu. A Jihar Ondo kuma, jami’an NDLEA bisa sahihan bayanan sirri sun kai samame dajin Itaogbolu, Akure, inda suka ƙwato kilo 351 na skunk da tsabarsa. Haka kuma, an kama Aminu Usman Gembu mai shekaru 66 a Aliade, Jihar Benuwai tare da kapsul 28,600 na tramadol.

A Jihar Edo, jami’an NDLEA sun kama Roland Owie mai shekaru 37 bayan samamen da suka kai rumbun ajiyarsa a Egbanke a ƙaramar hukumar Orhionmwon ranar Litinin 30 ga Maris, inda aka ƙwato kilo 1,378 na skunk.

Haka zalika, an kama wata shahararriyar dillaliyar miyagun ƙwayoyi, Ayantola Omodunmomi (Iya Elle) mai shekaru 40, a yankin Eleta na Ibadan, Jihar Oyo, ranar Laraba 1 ga Afrilu. An kama ta ne bayan bayanan sirri sun nuna yadda take amfani da ‘yarta mai shekaru 11, Anjola, wajen kai miyagun ƙwayoyi ga kwastomominta. A lokacin kamanta, an ƙwato kilo 45.6 na skunk daga rumbunta.

A ɓangaren wayar da kai, rundunonin NDLEA a faɗin ƙasar nan sun ci gaba da shirye-shiryen wayar da kai da yaƙi da shan miyagun ƙwayoyi (WADA) a makarantun, wuraren ibada da al’umma. Daga ciki akwai laccoci a makarantar Okere Grammar School, Saki (Oyo) da Shasha Comprehensiɓe High School, Alimosho (Legas) da Ma’ahad Ahmad Turaki Islamiyya, Sabon Gari (Kano) da Ezi-Awka Community Secondary School, Awka (Anambra) da Madrasatul Ihsan, Tsafe (Zamfara), da sauransu.

Yayin da yake yaba wa jami’an hukumar kan nasarorin da suka samu, Shugaban Hukumar NDLEA, Birgediya Janar Mohamed Buba Marwa (mai ritaya), ya jinjina wa jami’an hukumar a faɗin ƙasa kan ƙoƙarinsu na daidaita yaƙi da safarar miyagun ƙwayoyi da rage buƙatarsu.

NDLEA
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
Xi Jinping Ya Gana Da Cheng Li-Wun

Xi Jinping Ya Gana Da Cheng Li-Wun

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.