Jami’an Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Ƙasa (NDLEA) sun yi nasarar tarwatsa wata babbar ƙungiyar safarar miyagun ƙwayoyi bayan wani shiri na sirri da ya ɗauki tsawon makonni uku.
A yayin wannan aiki, an daƙile jigilar hodar ibilis da aka ɓoye cikin gwangwanin man ƙwarya da ake shirin tura wa zuwa ƙasar Birtaniya, tare da kai samame wurin da ake shirya kayan, lamarin da ya kai ga gano dukkan matakan ƙungiyar har zuwa kama jagoranta.
- Kwastam Ta Kama Miyagun Ƙwayoyi Na Naira Miliyan 99.9, Ta Miƙa Su Ga NDLEA A Sakkwato
- NDLEA Ta Kwace Kwayoyin Pregabalin 75,000 Da Hodar Iblis 556 A Kano
Nasaran ta fara ne tun a ranar da jami’an NDLEA da ke Ikeja a Jihar Legas suka gano kilo 3.10 na hodar ibilis a sashen fitar da kaya na filin jirgin sama. An ɓoye ƙwayar cikin gwangwanin kwakwar manja da aka shirya tura wa Birtaniya.
Nan take aka kama masu kula da kayan guda biyu da suka haɗa da Idris Olayiwola Amoo da Akinlami Akinsoji Adedoyin. Domin gano wanda ya aika da kayan da kuma jagoran ƙungiyar, jami’an suka gudanar da wani aiki na musamman ranar Alhamis 2 ga Afrilu wanda ya kai ga kama Ezemuwo Joel, wanda ke amfani da sunan ƙarya na Ajayi.
Kamen nasa ya kai jami’an ga jagoran ƙungiyar, King Arinze mai shekaru 52, wanda aka cafke a maboyarsa a yankin Isolo a Legas. Daga nan aka kai shi rumbun ajiyarsa da ke 11, Ola Ifa Street, Bucknor, Isolo, inda aka gano gwangwani 886 na kwakwar manja da aka shirya don ɓoye miyagun ƙwayoyi, da kayan aiki irinsu na’urar rufe gwangwani, masu buɗe gwangwani, fenti, gram 52 na cannabis satiɓa da safar hannu. Ya amsa cewa shi ne ke zubar da man daga gwangwanin domin ɓoye hodar ibilis.
A wani aiki daban a Jihar Borno, jami’an NDLEA a ranar Laraba 1 ga Afrilu sun kama wata mata mai bai wa ƙungiyoyin ƴan bindiga miyagun ƙwayoyi, Aisha Adamu mai shekaru 28, a kan titin Gamboru Ngala, ɗauke da kilo 4.3 na Colorado, wani nau’in tabar wiwi ta roba mai ƙarfi.
A gefe guda kuma, jami’an NDLEA sun kama faston cocin Celestial Church of Christ da ke Agonɓi Sea Beach, yankin Sakpo a Seme, Badagry, Fasto Afolabi Hodonu mai shekaru 45, tare da matarsa, Mrs. Success Hodonu mai shekaru 35, ranar Alhamis 2 ga Afrilu a shingen bincike na Gbaji. Binciken motarsu ƙirar Honda Pilot ya kai ga gano kilo 11 na skunk da aka ɓoye a sassan motar.
Kamen ma’auratan ya biyo bayan cafke wani da ya yi ƙaryar zama jami’in tsaro, Sunday Samuel mai shekaru 35, a wannan shingen ranar Litinin 30 ga Maris, ɗauke da kilo 24.5 na skunk daga Seme zuwa Legas.
A Jihar Adamawa, jami’an NDLEA da ke sintiri a kan titin Namtari, Yola ta kudu, ranar Litinin 30 ga Maris sun tare wata mota mai lamba RUW 947 ƊA ɗauke da ƙwayoyi 48,000 na tramadol. An kama direban, Abdulaziz Ismail Korede, yayin da bincike ya kai ga kama mai karɓar kayan, Idris Adamu.
A Jihar Osun, an kama Idiatu Oladejo mai shekaru 60 da kilo 15 na skunk a Isale Osun, Osogbo, ranar Laraba 1 ga Afrilu. A Jihar Ondo kuma, jami’an NDLEA bisa sahihan bayanan sirri sun kai samame dajin Itaogbolu, Akure, inda suka ƙwato kilo 351 na skunk da tsabarsa. Haka kuma, an kama Aminu Usman Gembu mai shekaru 66 a Aliade, Jihar Benuwai tare da kapsul 28,600 na tramadol.
A Jihar Edo, jami’an NDLEA sun kama Roland Owie mai shekaru 37 bayan samamen da suka kai rumbun ajiyarsa a Egbanke a ƙaramar hukumar Orhionmwon ranar Litinin 30 ga Maris, inda aka ƙwato kilo 1,378 na skunk.
Haka zalika, an kama wata shahararriyar dillaliyar miyagun ƙwayoyi, Ayantola Omodunmomi (Iya Elle) mai shekaru 40, a yankin Eleta na Ibadan, Jihar Oyo, ranar Laraba 1 ga Afrilu. An kama ta ne bayan bayanan sirri sun nuna yadda take amfani da ‘yarta mai shekaru 11, Anjola, wajen kai miyagun ƙwayoyi ga kwastomominta. A lokacin kamanta, an ƙwato kilo 45.6 na skunk daga rumbunta.
A ɓangaren wayar da kai, rundunonin NDLEA a faɗin ƙasar nan sun ci gaba da shirye-shiryen wayar da kai da yaƙi da shan miyagun ƙwayoyi (WADA) a makarantun, wuraren ibada da al’umma. Daga ciki akwai laccoci a makarantar Okere Grammar School, Saki (Oyo) da Shasha Comprehensiɓe High School, Alimosho (Legas) da Ma’ahad Ahmad Turaki Islamiyya, Sabon Gari (Kano) da Ezi-Awka Community Secondary School, Awka (Anambra) da Madrasatul Ihsan, Tsafe (Zamfara), da sauransu.
Yayin da yake yaba wa jami’an hukumar kan nasarorin da suka samu, Shugaban Hukumar NDLEA, Birgediya Janar Mohamed Buba Marwa (mai ritaya), ya jinjina wa jami’an hukumar a faɗin ƙasa kan ƙoƙarinsu na daidaita yaƙi da safarar miyagun ƙwayoyi da rage buƙatarsu.















Discussion about this post