Ƙungiyar ƴan kasuwa ta buƙaci gwamnatin tarayya da ta ware aƙalla kashi 60 cikin 100 na kuɗin ɗanyen mai domin tallafawa matatun mai na cikin gida, ciki har da Matatar Dangote, a wani yunƙuri na rage hauhawar farashin man fetur.
Shugaban ƙungiyar na ƙasa, Festus Osifo, ne ya bayyana hakan a Abuja, inda ya ce matakin zai taimaka wajen rage matsin tattalin arziƙin da ke ƙaruwa ga ‘yan Nijeriya, musamman duba da yadda farashin mai ya kai kusan naira 2,000 a kowace lita a wasu yankuna.
- An Cafke Yan Sudan Da Chadi 20 A Kano Bisa Shigo Wa Nijeria Ba Bisa Ka’ida Ba
- Dimokuradiyyar Dake Shafar Kowa a Sin Ingantaccen Karfi Ne Na Ingiza Shirin Raya Ci Gaban Sin Da Zamantakewar Al’umma Na Shekaru Biyar-Biyar Karo Na 15
Osifo ya ƙara da cewa hauhawar farashin ɗanyen mai sama da hasashen kasafin kuɗi na dala $64.85 a kowace ganga na samar da ƙarin kuɗaɗen shiga ga gwamnati a matakai daban-daban, amma hakan na iya kawo cikas ga ƙoƙarin rage hauhawar farashi da aka fara gani a baya-bayan nan.
Ya jaddada buƙatar ɗaukar matakan gaggawa tare da zuba jari na dogon lokaci a fannin makamashi, musamman amfani da iskar gas kamar CNG, da kuma sabunta na’urori da injuna domin rage dogaro da man fetur.
Haka kuma, ya nuna damuwa kan matsalar tsaro da ke addabar ƙasar, yana mai kira ga gwamnati da ta ƙara saka hannun jari a fasahar zamani da kayan aikin tsaro, tare da yaba wa hukumomin tsaro kan ƙoƙarin da suke yi.















Discussion about this post