ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ci Gaban Sin Zai Haifar Da Ci Gaban Afirka

by Sulaiman
6 months ago

“Ci gaban kasashen duniya, ya kasance tushen ci gaban kasar Sin. Kana ci gaban Sin shi ma zai haifar da ci gaba a duniya.” Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya taba bayyana alakar dake tsakanin kasarsa da duniya kamar haka. To, idan mun takaita abubuwan da maganar ta shafa zuwa alakar dake tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka, za mu ga hakan ma abun yake, wato ci gaban kasar Sin zai haifar da ci gaban kasashen Afirka. Hakika, ba wani abu mai wuya ba ne, idan ana son neman shaidu da za su tabbatar da gaskiyar maganar, ta hanyar karanta jawabin taya murnar sabuwar shekara da shugaba Xi Jinping ya gabatar, a kwanan nan, tare da gudanar da tsokaci a kansa.

Cikin jawabinsa, shugaba Xi ya ambaci nasarorin da kasar Sin ta samu a fannin raya kasa. Cikin shekarar da ta shude, an sa ran cewa, jimillar GDPn kasar a mizanin duk shekara za ta kai kimanin kudin Sin Yuan triliyan 140, kwatankwacin dalar Amurka triliyan 20, jimillar da ta shaida karuwar karfin kasar a fannin tattalin arziki. To, karanta bayanin ya sa ni tunawa da karuwar cinikin da ake yi tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka a bara. An ce, tun daga watan Janairu zuwa na Nuwamban shekarar 2025, darajar cinikin da aka yi tsakanin Sin da Afirka ta zarce dalar Amurka biliyan 300 a karon farko a tarihi, ta yadda kasar Sin ta kiyaye matsayinta na kawar ciniki mafi girma ta nahiyar Afirka wasu shekaru 16 a jere. Ban da haka, duk a cikin shekarar 2025, kasar Sin ta kulla yarjejeniyar hadin gwiwa, karkashin tsarin Ziri Daya da Hanya Daya, tare da karin kasashe, irinsu Kenya da Sudan ta Kudu. Kana ta kaddamar da aikin zamanantar da layin dogon da ya hada Tanzania da Zambia, da ci gaba da kokarin sabunta tashar jiragen ruwa ta Nacala dake kasar Mozambique, a kokarin karfafa tushen bangaren sufuri ga ci gaban nahiyar Afrika. To, tantance wadannan abubuwa zai sa mutum fahimtar cewa, ci gaban kasar Sin tana sa kaimi ga ci gaban tattalin arzikin kasashen Afirka.

Ban da haka, shugaba Xi Jinping na kasar Sin, a cikin jawabinsa na murnar sabuwar shekara, ya ce kasarsa ta zama daya daga cikin kasashe mafi ci gaban fannin kimiyya da fasaha. To, maganarsa ta tunatar da ni game da kalmomin da Gaspard Banyankimbona, wani babban jami’in kungiyar tarayyar kasashen Afirka (AU) ya fada, wajen wani taron da ya gudana a birnin Wuhan na kasar Sin a watan Nuwamban bara, inda ya ce, sabbin fasahohin kasar Sin suna haifar da alfanu ga al’ummun kasashen Afirka, misali manhajojin biya kudi suna saukaka ayyukan hada-hadar kudi a Afirka, kana allunan samar da wutar lantarki ta hasken rana suna taimakon kokarin zamanantar da kauyukan Afirka. Hakika, dimbin shaidu sun nuna cewa, ci gaban kimiyya da fasaha a kasar Sin yana karfafa jin dadin rayuwar al’ummun kasashen Afirka.

ADVERTISEMENT

Sa’an nan, ban da ci gaban Sin a fannonin tattalin arziki, da kimiyya da fasaha, manufofinta su ma suna amfanar da kasashen Afirka. Misali, a cikin jawabinsa na murnar sabuwar shekara, shugaba Xi Jinping na Sin ya ambaci yadda kasarsa ke kara bude kofa ga kasashen ketare, maganar da ta sa na tuna da yadda a shekarar 2025, kasar ta Sin ta sanar da shirinta na yafe wa kasashe 53 dake nahiyar Afirka, wadanda suka kulla huldar diflomasiyya da ita, harajin kwastam. Dangane da batun, shahararren masani dan Najeriya, Charles Onunaiju, ya ce, manufar da kasar Sin ta gabatar za ta daidaita tsare-tsaren tattalin arzikin daukacin nahiyar Afirka, inda za a ba kasashen Afirka damar fitar da karin kayayyaki, da samun karin kudin shiga, da karfafa tasirin yankin ciniki maras shinge na nahiyar Afirka, ta hanyar ingiza bangaren samar da kayayyaki masu daraja, da dunkulewar shiyyoyin Afirka ta fuskar tattalin arziki da ciniki.

Duk a cikin jawabinsa na taya murnar sabuwar shekara, shugaba Xi Jinping ya ambaci shawarar inganta jagorancin duniya (GGI) da ya gabatar a shekarar bara, don neman kara tabbatar da adalci a duniya. Dangane da batun, na tuna da wani bayanin da wani masani mai suna Hildebrand Shayo, dan kasar Tanzania, ya rubuta, wanda a cikin makalarsa ya ce, yadda shawarar GGI ta dora muhimmanci kan daidaituwar ikon mulkin kai na mabambantan kasashe, wanda hakan zai haifar da alfanu ga kasashen Afirka, wadanda suka dade suna jin radadin matsalar rashin daidaito a tsare-tsaren duniya.

LABARAI MASU NASABA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

A karshen jawabinsa, shugaba Xi na kasar Sin ya karfafa gwiwar jama’a domin su kara kokarin aiki a hadin gwiwarsu, ta yadda za su samu damar cika dukkan burikan da suka sanya a gaba. To, wannan fatan alheri, a ganina, tabbas zai tabbatar da makomar huldar Sin da Afirka a sabuwar shekara ta 2026 da muke ciki. (Bello Wang)

Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Next Post
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 51, 876 Sun Mika Wuya A Arewa Maso Gabas

Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Jihar Kano

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.