ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ci Gaban Sin Zai Haifar Da Ci Gaban Afirka

by Sulaiman
8 months ago

“Ci gaban kasashen duniya, ya kasance tushen ci gaban kasar Sin. Kana ci gaban Sin shi ma zai haifar da ci gaba a duniya.” Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya taba bayyana alakar dake tsakanin kasarsa da duniya kamar haka. To, idan mun takaita abubuwan da maganar ta shafa zuwa alakar dake tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka, za mu ga hakan ma abun yake, wato ci gaban kasar Sin zai haifar da ci gaban kasashen Afirka. Hakika, ba wani abu mai wuya ba ne, idan ana son neman shaidu da za su tabbatar da gaskiyar maganar, ta hanyar karanta jawabin taya murnar sabuwar shekara da shugaba Xi Jinping ya gabatar, a kwanan nan, tare da gudanar da tsokaci a kansa.

Cikin jawabinsa, shugaba Xi ya ambaci nasarorin da kasar Sin ta samu a fannin raya kasa. Cikin shekarar da ta shude, an sa ran cewa, jimillar GDPn kasar a mizanin duk shekara za ta kai kimanin kudin Sin Yuan triliyan 140, kwatankwacin dalar Amurka triliyan 20, jimillar da ta shaida karuwar karfin kasar a fannin tattalin arziki. To, karanta bayanin ya sa ni tunawa da karuwar cinikin da ake yi tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka a bara. An ce, tun daga watan Janairu zuwa na Nuwamban shekarar 2025, darajar cinikin da aka yi tsakanin Sin da Afirka ta zarce dalar Amurka biliyan 300 a karon farko a tarihi, ta yadda kasar Sin ta kiyaye matsayinta na kawar ciniki mafi girma ta nahiyar Afirka wasu shekaru 16 a jere. Ban da haka, duk a cikin shekarar 2025, kasar Sin ta kulla yarjejeniyar hadin gwiwa, karkashin tsarin Ziri Daya da Hanya Daya, tare da karin kasashe, irinsu Kenya da Sudan ta Kudu. Kana ta kaddamar da aikin zamanantar da layin dogon da ya hada Tanzania da Zambia, da ci gaba da kokarin sabunta tashar jiragen ruwa ta Nacala dake kasar Mozambique, a kokarin karfafa tushen bangaren sufuri ga ci gaban nahiyar Afrika. To, tantance wadannan abubuwa zai sa mutum fahimtar cewa, ci gaban kasar Sin tana sa kaimi ga ci gaban tattalin arzikin kasashen Afirka.

Ban da haka, shugaba Xi Jinping na kasar Sin, a cikin jawabinsa na murnar sabuwar shekara, ya ce kasarsa ta zama daya daga cikin kasashe mafi ci gaban fannin kimiyya da fasaha. To, maganarsa ta tunatar da ni game da kalmomin da Gaspard Banyankimbona, wani babban jami’in kungiyar tarayyar kasashen Afirka (AU) ya fada, wajen wani taron da ya gudana a birnin Wuhan na kasar Sin a watan Nuwamban bara, inda ya ce, sabbin fasahohin kasar Sin suna haifar da alfanu ga al’ummun kasashen Afirka, misali manhajojin biya kudi suna saukaka ayyukan hada-hadar kudi a Afirka, kana allunan samar da wutar lantarki ta hasken rana suna taimakon kokarin zamanantar da kauyukan Afirka. Hakika, dimbin shaidu sun nuna cewa, ci gaban kimiyya da fasaha a kasar Sin yana karfafa jin dadin rayuwar al’ummun kasashen Afirka.

ADVERTISEMENT

Sa’an nan, ban da ci gaban Sin a fannonin tattalin arziki, da kimiyya da fasaha, manufofinta su ma suna amfanar da kasashen Afirka. Misali, a cikin jawabinsa na murnar sabuwar shekara, shugaba Xi Jinping na Sin ya ambaci yadda kasarsa ke kara bude kofa ga kasashen ketare, maganar da ta sa na tuna da yadda a shekarar 2025, kasar ta Sin ta sanar da shirinta na yafe wa kasashe 53 dake nahiyar Afirka, wadanda suka kulla huldar diflomasiyya da ita, harajin kwastam. Dangane da batun, shahararren masani dan Najeriya, Charles Onunaiju, ya ce, manufar da kasar Sin ta gabatar za ta daidaita tsare-tsaren tattalin arzikin daukacin nahiyar Afirka, inda za a ba kasashen Afirka damar fitar da karin kayayyaki, da samun karin kudin shiga, da karfafa tasirin yankin ciniki maras shinge na nahiyar Afirka, ta hanyar ingiza bangaren samar da kayayyaki masu daraja, da dunkulewar shiyyoyin Afirka ta fuskar tattalin arziki da ciniki.

Duk a cikin jawabinsa na taya murnar sabuwar shekara, shugaba Xi Jinping ya ambaci shawarar inganta jagorancin duniya (GGI) da ya gabatar a shekarar bara, don neman kara tabbatar da adalci a duniya. Dangane da batun, na tuna da wani bayanin da wani masani mai suna Hildebrand Shayo, dan kasar Tanzania, ya rubuta, wanda a cikin makalarsa ya ce, yadda shawarar GGI ta dora muhimmanci kan daidaituwar ikon mulkin kai na mabambantan kasashe, wanda hakan zai haifar da alfanu ga kasashen Afirka, wadanda suka dade suna jin radadin matsalar rashin daidaito a tsare-tsaren duniya.

LABARAI MASU NASABA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

A karshen jawabinsa, shugaba Xi na kasar Sin ya karfafa gwiwar jama’a domin su kara kokarin aiki a hadin gwiwarsu, ta yadda za su samu damar cika dukkan burikan da suka sanya a gaba. To, wannan fatan alheri, a ganina, tabbas zai tabbatar da makomar huldar Sin da Afirka a sabuwar shekara ta 2026 da muke ciki. (Bello Wang)

Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara
  • Sulaiman
    Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan
  • Sulaiman
    ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

MASU ALAKA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta
Ra'ayi Riga

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

September 8, 2026
Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

September 4, 2026
Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa
Ra'ayi Riga

Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa

September 2, 2026
Next Post
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 51, 876 Sun Mika Wuya A Arewa Maso Gabas

Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Jihar Kano

LABARAI MASU NASABA

Yaya Toure Na Dab Da Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai

Yaya Toure Na Dab Da Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai

September 9, 2026
’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.