Masu shirin gudanar da Umrah na iya fuskantar ƙarin kuɗi bayan ƙaddamar da sabon tsarin tikitin abinci na Nusuk wanda ya zama wajibi ga dukkan alhazan Umrah. Sabon tsarin zai haɗa kuɗin tikitin abincin kai tsaye cikin kuɗin bizar Umrah.
A ƙarƙashin tsarin, wanda zai fara aiki daga 1 ga Rabi’ul Awwal, kowane mahajjacin Umrah zai riƙa biyan Riyal 20 na Saudiyya (SAR) a kowace rana domin tikitin abinci na Nusuk. Ba za a karɓi wannan kuɗi dabam ba, domin za a haɗa shi ne cikin kuɗin bizar.
A matakin farko, za a fara aiwatar da tsarin ne a ƙasashe huɗu da suka haɗa da Pakistan, Indiya, Bangladesh da Masar, kafin daga bisani a faɗaɗa shi zuwa sauran ƙasashe.
Bayanan tsarin sun nuna cewa tikitin abincin zai yi aiki kamar yadda ake gudanar da sabis na sufuri a manhajar Nusuk. Za a ƙididdige kuɗin gwargwadon kwanakin da mahajjaci zai yi a Saudiyya, sannan a tabbatar da biyan kuɗin kafin a ba shi bizar Umrah.
Haka kuma, sama da gidajen cin abinci 10,000 da ke haɗe da manhajar Nusuk ne za su iya karɓi tikitin domin bai wa alhazai damar cin gajiyar tsarin yayin zamansu a ƙasar Saudiyya.














