Cibiyar nazari da bincike ta kasar Zimbabwe, Southern African Research and Documentation Center (SARDC), ta yi kira da a sanya cibiyoyin nazari bincike a manyan batutuwan hadin gwiwa tsakain kasar Sin da Africa, domin inganta tattaunawa, bunkasa kirkire-kirkire da neman tabbatar da ci gaba mai dorewa.
Da yake jawabi a jiya Alhamis biyo bayan rattaba hannu kan yarjejeniyar fahimatar juna da jami’ar Xiangtan ta kasar Sin, babban daraktan cibiyar SARDC Joseph Ngwawi ya bayyana cewa, kawance tsakanin SARDC da jami’ar Xiangtan ya nuna cigaba mai karfi da za a samu ta fuskar baiwa ilmi da bincike muhimmanci a yarjejeniyar da aka kulla da kasar Sin.
Ngwawi ya kara da cewa cibiyar SARDC ba wai tana kallon alakar da aka kulla a matsayin yarjejeniya kawai ba, sai dai a matsayin wani kyakkyawan bigire da dabaru na karfafa alakar kasashen Zimbabwe da Sin, da kuma bunkasa hadin gwiwa tsakanin Africa da Sin.
Shugaban jami’ar Xiangtan Liao Yong’an, wanda ya samu wakilcin wani manazarci kuma malami a jami’ar, da ke karkashin cibiyar nazari da bincike ta Africa da Sin, Wang Weifeng, ya bayyana alakar da aka kulla a matsayin mafari, kamar yadda SARDC ta fitar.
Liao ya kara da cewa, ana fatan wannan yarjejeniya za ta haifar da hadin gwiwa mai karfi a nan gaba, wanda zai hada da hada hannu wajen nazari da bincike, da musayar harkokin ilmi, da shirya tarukan karawa juna sani da kuma musayar ilmi da kwarewa tsakanin malamai da dalibai. (Suleiman Suleiman Ibrahim)














