ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cin Zali Ba Zai Iya Hana Kasashen Afirka Ci Gaba Ba

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Afirka

Minista mai kula da masana’antu, ciniki da zuba jari ta kasar Najeriya, Jumoke Oduwole, ta fada a jiya Lahadi cewa, matakin karbar karin harajin kwastam da kasar Amurka ta yi shirin dauka, zai yi mummunan tasiri kan fitar da kayayyakin Najeriya zuwa kasar Amurka, da lalata huldar ciniki dake tsakanin kasashen 2.

Hakika yawan harajin kwastam na kaso 14% da kasar Amurka za ta kakaba wa kasar Najeriya bai kai adadin harajin da Amurka din ta sanya wa sauran kasashe dake nahiyar Afirka ba, idan an kwatanta da kaso 47% na kasar Madagascar, da 40% na Mauritius, da 37% na Botswana, da 30% na Afirka ta Kudu, da dai sauransu. Kana abun mamaki shi ne, kasar da Amurka za ta karbi mafi yawan haraji bisa kayayyakinta a nahiyar Afirka ita ce Lesotho, ko da yake karamar kasa ce mai fama da koma bayan tattalin arziki, inda yawan harajin da Amurka za ta kakabawa kasar zai kai kaso 50%.

  • INEC Ta Musanta Korar Farfesa Yakubu A Matsayin Shugaban Hukumar
  • Harin Filato: An kashe Mutane 40, An Kona Gidaje 383, Fiye Da Mutane 1,000 An Raba Su Da Muhallansu 

Da ma dokar Amurka ta tabbatar da ci gaban kasashen Afirka (AGOA) ta ba wasu kasashen dake nahiyar Afirka damar fitar da kayayyakinsu zuwa kasar Amurka, ba tare da bukatar biyan harajin kwastam ba. Amma yanzu, matakin karbar karin haraji da kasar Amurka ta shirya dauka ya nuna cewa za a ga bayan dokar nan ta AGOA. A cewar wani shahararren lauya na kasar Birtaniya mai suna Colette Ven, matakin kasar Amurka tamkar yanke hukunci ne kan kasashen Afirka, bisa ribar da suka taba samu sakamakon dokar AGOA din.

ADVERTISEMENT

 

Ban da haka, a ganin masana na kasashe daban daban, munufar haraji ta kasar Amurka ta keta ka’idojin kungiyar ciniki ta duniya WTO, da bijirewa bambancin karfin tattalin arziki na kasashe daban daban. Inda kasar take neman cin zalin kasashen duniya, da hana ci gaban tattalin arzikin kasashe masu tasowa.

LABARAI MASU NASABA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

 

A nata bangare, ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ita ma ta sanar da cewa, kowace kasa na da hakkin neman ci gaba, saboda haka bai kamata a ba wasu kasashe damar yin babakere ba. Ganin yadda kasar Amurka ke neman dora moriyarta a kan hakkin kasashen duniya, ya sa kasar Sin kin amincewa da matakinta.

 

Yanzu haka ra’ayin kasar Sin na samun amincewa daga mutanen kasashe daban daban. Bisa sakamakon binciken ra’ayin jama’a da kafar watsa labarai ta kasar Sin CGTN ta gudanar, cikin mutanen kasashe daban daban da aka yi musu tambayoyi, kaso 86.9% sun ce matakan ramuwar gayya da kasashe daban daban suka dauka bisa matakin karbar karin haraji na kasar Amurka, sun halatta, kana kaso 87.7% na mutanen sun ce ya kamata kasashe daban daban su yi hadin gwiwa, a kokarin dakile matakin Amurka na cin zarafin sauran kasashe.

 

A nahiyar Afirka ma, matakin Amurka ya janyo sabon tunani kan dabarar raya kasa. Inda masanin ilimin shari’a na kasar Najeriya Livingstone Wechie ya ce, ko da yake kasar Amurka ta taba alkawarin raya masana’antu a kasashen Afirka karkashin dokar AGOA, sakamako na karshe ya nuna cewa ta yi karya ke nan. Saboda haka mista Wechie ya ce dogara kan tallafin da ake samu daga kasashen waje ba zai raya tattalin arzikin kasashen Afirka yadda suke bukata ba.

 

Kana a ganin masaniyar ilimin tattalin arziki ‘yar kasar Afirka ta Kudu, Annabel Bishop, cin zalin da kasar Amurka ke yi, zai sa kasashen Afirka gaggauta karkata ga abokan hulda dake kan hanyar tasowa wajen gudanar da ciniki.

 

Ban da haka, Leseko Makhetha, masanin ilimin tattalin arziki na kasar Lesotho, ya ce matsin lambar da kasar Amurka ta yi wa kasashen Afirka, za ta sa su kara kokarin gina yankin ciniki mai ‘yanci na nahiyar Afirka.

 

Yayin da a nata bangare, minista mai kula da masana’antu, ciniki da zuba jari ta kasar Najeriya, Jumoke Oduwole, ta ce matakin matsin lamba na Amurka ya sa Najeriya tabbatar da niyyar raya bangaren fitar da kayayyakin da ba su shafi danyen mai ba. A cewarta, Najeriya za ta yi kokarin inganta kayayyakinta, don neman sayar da su a karin kasuwannin kasashe daban daban.

 

Amurka na son toshe hanyar neman ci gaban tattalin arziki ta kasashen Afirka, da ta sauran kasashe masu tasowa na nahiyoyi daban daban. Sai dai ba za ta samu biyan bukata ba. Saboda matakin cin zalin ba zai haifar da komai ba, illa farkarwa, da dogaro da kai, da karfin zuci, da hadin kai, ga kasashe daban daban. Tabbas rinjayen kasashe, wadanda suke da adalci, za su ci nasara a karshe, a wannan gasar da ake gudanar da ita a duniya. (Bello Wang)

Afirka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
Afirka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki
Ra'ayi Riga

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

June 3, 2026
Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka
Ra'ayi Riga

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

June 1, 2026
Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya

May 29, 2026
Next Post
Matakin Sin Na Karfafa Takaita Fitar Da Abubuwa Masu Alaka Da Ma’adanan “Rare Rarth” Na Nuni Ga Aniyarta Ta Kare Tsaron Kasa

Matakin Sin Na Karfafa Takaita Fitar Da Abubuwa Masu Alaka Da Ma’adanan “Rare Rarth” Na Nuni Ga Aniyarta Ta Kare Tsaron Kasa

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.