ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 21, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 days ago
Sin

A Bangaren Kiwon Lafiya Kwanan nan, babban darektan cibiyar kandagarkin cututtuka ta Afirka wato Africa CDC Dr. Jean Kaseya ya bayyana cewa, Sin ta ba da tallafi mai karfi wajen taimaka wa kasashen Afirka tinkarar cutar Ebola a wannan karo, a fannonin tura ma’aikatanta da samar da kayayyaki da sauransu. Sin babbar kawar kasashen Afirka ce, kuma cibiyar tana fatan kara karfafa hadin gwiwa da ita.

Hukumar lafiya ta duniya WHO ta ayyana cutar Ebola da ta barke a Jamhuriyar Dimokuradiyyar Kongo da Uganda a wannan karo, a matsayin “matsalar lafiya da ke bukatar daukin gaggawa daga kasashen duniya”. Duba da hakan, kungiyar kwararrun likitocin Sin ta tashi daga birnin Beijing da sanyin safiyar ranar 2 ga watan Yuni cikin gaggawa, don taimaka wa nahiyar Afirka wajen yaki da cutar Ebola, inda za su gudanar da ayyuka na tsawon watanni uku.

Yawan mace-macen masu kamuwa da Ebola ya kan kai kashi 30 zuwa 90, kuma cuta ce mai saurin yaduwa, lamarin da ya sa shawo kanta ya zama aiki mai wuya. A cikin irin wannan hali ne, kungiyar kwararrun likitoci na kasar Sin da ta samu umurni sai ta tashi nan da nan zuwa Kinshasa ba tare da bata lokaci ba, kuma sun je tare da kayayyakin kandagarki da ake matukar bukata.

ADVERTISEMENT

Wannan ba shi ne karo na farko da Sin ta ba da taimako irin haka ba. A shekara ta 2014, lokacin da cutar Ebola ta jefa Afirka cikin mawuyancin hali, duniya ta shiga tsoron cutar, kuma kasashe da yawa suka janye kungiyoyin likitocinsu da ke Afirka, amma kasar Sin a nata bangare ta tura kungiyar likitocinta zuwa yankin da cutar ta shafa don ba da taimako. Bayan barkewar cutar a bana, tawagar likitocin Sin ta 24 da ke aiki a Kongo Kinshasa, ta dauki matakan gaggawa nan take. Kamar yadda masanin cututtuka na Kongo Kinshasa Jean-Jacques Muyembe ya ce, “Sai a lokacin wahala ake gane aboki na gaske.”Abin lura shi ne, tallafin da Sin ta bayar na yaki da cutar a Afirka ba “taimako na gaggawa” ba ne kawai.

Jagoran kungiyar kwararrun likitocin da kasar Sin ta tura zuwa Congo Kinshasa a wannan karo Lu Ming ya bayyana cewa, manufarsu ita ce taimakawa yankin wajen inganta karfinsu na yaki da cutar Ebola da kuma kiwon lafiya. A Uganda, tawagar likitocin Sin ta 25 da ke kasar ta taimaka wa asibitin sada zumunta na Sin da Uganda wajen inganta tsarinsa na tantance cututtuka da kuma rarraba marasa lafiya, tare da more dabarun kasar Sin wajen hana yaduwar cututtuka.Tun lokacin da Sin ta aika tawagar likitocinta ta farko zuwa Aljeriya a shekara ta 1963 zuwa yanzu, kasar ta tura ma’aikatan lafiya sama da 26,000 zuwa kasashen Afirka 48, inda suka samar da jiyya ga marasa lafiya sama da miliyan 230.

LABARAI MASU NASABA

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

Daga Taklamakan Zuwa Sahara: Yadda Hamada Ke “Haifar” Da Fata

A halin yanzu, ma’aikatan lafiya 900 da ke cikin tawagogin likitoci 45 da Sin ta tura kasashen Afirka 44 suna gudanar da ayyukansu yadda ya kamata. Za a magance cutar Ebola wata rana, amma hadin gwiwar sha’anin kiwon lafiyar jama’a tsakanin Sin da Afirka ba za ta tsaya ba.

Daga tura kungiyoyin likitoci zuwa gina cibiyoyin magance cututtuka, daga koyar da fasaha zuwa horar da ma’aikata, abubuwan da Sin ke yi ba “samar da taimakon gaggawa” ba ne kadai, yana kuma taimaka wa Afirka wajen gina ingantaccen tsarin kiwon lafiyar jama’ar nahiyar. Kamar yadda mataimakin firaministan kasar Sin Liu Guozhong ya fada a taron koli na musamman kan yaki da cutar Ebola da aka gudanar ta bidiyo a baya-bayan nan: “Sin da Afirka na da makomar bai daya.” Hakan ya sa, Sin take daukar hakikanan ingantattun matakai don gina kyakkaywar makomar al’ummar Sin da Afirka ta bai daya a bangaren kiwon lafiya.(Marubuciya: MINA)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Sulaiman
    FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa
  • Sulaiman
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Sulaiman
    Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba

MASU ALAKA

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Daga Taklamakan Zuwa Sahara: Yadda Hamada Ke “Haifar” Da Fata
Ra'ayi Riga

Daga Taklamakan Zuwa Sahara: Yadda Hamada Ke “Haifar” Da Fata

June 17, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci
Ra'ayi Riga

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
Next Post
Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi

Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi

June 21, 2026
FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa

FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa

June 21, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran

Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran

June 21, 2026
‘Yan Wasa 23 Da Eric Chelle Ya Gayyata Domin Buga Wasannin Sada Zumunci 

Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba

June 20, 2026
Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

June 20, 2026
Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)

Hijira: Malaman Musulunci Sun Buƙaci  Musulmi Su Yi Riƙo Da Gaskiya Da Adalci

June 20, 2026
Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

June 20, 2026
Nijeriya

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai

Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai

June 20, 2026
Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno

Sojoji Sun Ceto Mutane 22 A Jihar Sakkwato

June 20, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.