A Bangaren Kiwon Lafiya Kwanan nan, babban darektan cibiyar kandagarkin cututtuka ta Afirka wato Africa CDC Dr. Jean Kaseya ya bayyana cewa, Sin ta ba da tallafi mai karfi wajen taimaka wa kasashen Afirka tinkarar cutar Ebola a wannan karo, a fannonin tura ma’aikatanta da samar da kayayyaki da sauransu. Sin babbar kawar kasashen Afirka ce, kuma cibiyar tana fatan kara karfafa hadin gwiwa da ita.
Hukumar lafiya ta duniya WHO ta ayyana cutar Ebola da ta barke a Jamhuriyar Dimokuradiyyar Kongo da Uganda a wannan karo, a matsayin “matsalar lafiya da ke bukatar daukin gaggawa daga kasashen duniya”. Duba da hakan, kungiyar kwararrun likitocin Sin ta tashi daga birnin Beijing da sanyin safiyar ranar 2 ga watan Yuni cikin gaggawa, don taimaka wa nahiyar Afirka wajen yaki da cutar Ebola, inda za su gudanar da ayyuka na tsawon watanni uku.
Yawan mace-macen masu kamuwa da Ebola ya kan kai kashi 30 zuwa 90, kuma cuta ce mai saurin yaduwa, lamarin da ya sa shawo kanta ya zama aiki mai wuya. A cikin irin wannan hali ne, kungiyar kwararrun likitoci na kasar Sin da ta samu umurni sai ta tashi nan da nan zuwa Kinshasa ba tare da bata lokaci ba, kuma sun je tare da kayayyakin kandagarki da ake matukar bukata.
Wannan ba shi ne karo na farko da Sin ta ba da taimako irin haka ba. A shekara ta 2014, lokacin da cutar Ebola ta jefa Afirka cikin mawuyancin hali, duniya ta shiga tsoron cutar, kuma kasashe da yawa suka janye kungiyoyin likitocinsu da ke Afirka, amma kasar Sin a nata bangare ta tura kungiyar likitocinta zuwa yankin da cutar ta shafa don ba da taimako. Bayan barkewar cutar a bana, tawagar likitocin Sin ta 24 da ke aiki a Kongo Kinshasa, ta dauki matakan gaggawa nan take. Kamar yadda masanin cututtuka na Kongo Kinshasa Jean-Jacques Muyembe ya ce, “Sai a lokacin wahala ake gane aboki na gaske.”Abin lura shi ne, tallafin da Sin ta bayar na yaki da cutar a Afirka ba “taimako na gaggawa” ba ne kawai.
Jagoran kungiyar kwararrun likitocin da kasar Sin ta tura zuwa Congo Kinshasa a wannan karo Lu Ming ya bayyana cewa, manufarsu ita ce taimakawa yankin wajen inganta karfinsu na yaki da cutar Ebola da kuma kiwon lafiya. A Uganda, tawagar likitocin Sin ta 25 da ke kasar ta taimaka wa asibitin sada zumunta na Sin da Uganda wajen inganta tsarinsa na tantance cututtuka da kuma rarraba marasa lafiya, tare da more dabarun kasar Sin wajen hana yaduwar cututtuka.Tun lokacin da Sin ta aika tawagar likitocinta ta farko zuwa Aljeriya a shekara ta 1963 zuwa yanzu, kasar ta tura ma’aikatan lafiya sama da 26,000 zuwa kasashen Afirka 48, inda suka samar da jiyya ga marasa lafiya sama da miliyan 230.
A halin yanzu, ma’aikatan lafiya 900 da ke cikin tawagogin likitoci 45 da Sin ta tura kasashen Afirka 44 suna gudanar da ayyukansu yadda ya kamata. Za a magance cutar Ebola wata rana, amma hadin gwiwar sha’anin kiwon lafiyar jama’a tsakanin Sin da Afirka ba za ta tsaya ba.
Daga tura kungiyoyin likitoci zuwa gina cibiyoyin magance cututtuka, daga koyar da fasaha zuwa horar da ma’aikata, abubuwan da Sin ke yi ba “samar da taimakon gaggawa” ba ne kadai, yana kuma taimaka wa Afirka wajen gina ingantaccen tsarin kiwon lafiyar jama’ar nahiyar. Kamar yadda mataimakin firaministan kasar Sin Liu Guozhong ya fada a taron koli na musamman kan yaki da cutar Ebola da aka gudanar ta bidiyo a baya-bayan nan: “Sin da Afirka na da makomar bai daya.” Hakan ya sa, Sin take daukar hakikanan ingantattun matakai don gina kyakkaywar makomar al’ummar Sin da Afirka ta bai daya a bangaren kiwon lafiya.(Marubuciya: MINA)















Discussion about this post