ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 weeks ago
Sin

A Bangaren Kiwon Lafiya Kwanan nan, babban darektan cibiyar kandagarkin cututtuka ta Afirka wato Africa CDC Dr. Jean Kaseya ya bayyana cewa, Sin ta ba da tallafi mai karfi wajen taimaka wa kasashen Afirka tinkarar cutar Ebola a wannan karo, a fannonin tura ma’aikatanta da samar da kayayyaki da sauransu. Sin babbar kawar kasashen Afirka ce, kuma cibiyar tana fatan kara karfafa hadin gwiwa da ita.

Hukumar lafiya ta duniya WHO ta ayyana cutar Ebola da ta barke a Jamhuriyar Dimokuradiyyar Kongo da Uganda a wannan karo, a matsayin “matsalar lafiya da ke bukatar daukin gaggawa daga kasashen duniya”. Duba da hakan, kungiyar kwararrun likitocin Sin ta tashi daga birnin Beijing da sanyin safiyar ranar 2 ga watan Yuni cikin gaggawa, don taimaka wa nahiyar Afirka wajen yaki da cutar Ebola, inda za su gudanar da ayyuka na tsawon watanni uku.

Yawan mace-macen masu kamuwa da Ebola ya kan kai kashi 30 zuwa 90, kuma cuta ce mai saurin yaduwa, lamarin da ya sa shawo kanta ya zama aiki mai wuya. A cikin irin wannan hali ne, kungiyar kwararrun likitoci na kasar Sin da ta samu umurni sai ta tashi nan da nan zuwa Kinshasa ba tare da bata lokaci ba, kuma sun je tare da kayayyakin kandagarki da ake matukar bukata.

ADVERTISEMENT

Wannan ba shi ne karo na farko da Sin ta ba da taimako irin haka ba. A shekara ta 2014, lokacin da cutar Ebola ta jefa Afirka cikin mawuyancin hali, duniya ta shiga tsoron cutar, kuma kasashe da yawa suka janye kungiyoyin likitocinsu da ke Afirka, amma kasar Sin a nata bangare ta tura kungiyar likitocinta zuwa yankin da cutar ta shafa don ba da taimako. Bayan barkewar cutar a bana, tawagar likitocin Sin ta 24 da ke aiki a Kongo Kinshasa, ta dauki matakan gaggawa nan take. Kamar yadda masanin cututtuka na Kongo Kinshasa Jean-Jacques Muyembe ya ce, “Sai a lokacin wahala ake gane aboki na gaske.”Abin lura shi ne, tallafin da Sin ta bayar na yaki da cutar a Afirka ba “taimako na gaggawa” ba ne kawai.

Jagoran kungiyar kwararrun likitocin da kasar Sin ta tura zuwa Congo Kinshasa a wannan karo Lu Ming ya bayyana cewa, manufarsu ita ce taimakawa yankin wajen inganta karfinsu na yaki da cutar Ebola da kuma kiwon lafiya. A Uganda, tawagar likitocin Sin ta 25 da ke kasar ta taimaka wa asibitin sada zumunta na Sin da Uganda wajen inganta tsarinsa na tantance cututtuka da kuma rarraba marasa lafiya, tare da more dabarun kasar Sin wajen hana yaduwar cututtuka.Tun lokacin da Sin ta aika tawagar likitocinta ta farko zuwa Aljeriya a shekara ta 1963 zuwa yanzu, kasar ta tura ma’aikatan lafiya sama da 26,000 zuwa kasashen Afirka 48, inda suka samar da jiyya ga marasa lafiya sama da miliyan 230.

LABARAI MASU NASABA

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

A halin yanzu, ma’aikatan lafiya 900 da ke cikin tawagogin likitoci 45 da Sin ta tura kasashen Afirka 44 suna gudanar da ayyukansu yadda ya kamata. Za a magance cutar Ebola wata rana, amma hadin gwiwar sha’anin kiwon lafiyar jama’a tsakanin Sin da Afirka ba za ta tsaya ba.

Daga tura kungiyoyin likitoci zuwa gina cibiyoyin magance cututtuka, daga koyar da fasaha zuwa horar da ma’aikata, abubuwan da Sin ke yi ba “samar da taimakon gaggawa” ba ne kadai, yana kuma taimaka wa Afirka wajen gina ingantaccen tsarin kiwon lafiyar jama’ar nahiyar. Kamar yadda mataimakin firaministan kasar Sin Liu Guozhong ya fada a taron koli na musamman kan yaki da cutar Ebola da aka gudanar ta bidiyo a baya-bayan nan: “Sin da Afirka na da makomar bai daya.” Hakan ya sa, Sin take daukar hakikanan ingantattun matakai don gina kyakkaywar makomar al’ummar Sin da Afirka ta bai daya a bangaren kiwon lafiya.(Marubuciya: MINA)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Ta Fitar Da Shirin Kai Wa Matakin Koli Na Fitar Da Hayakin Carbon
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Yi Nasarar Dawo Da Rokar Da Ake Sarrafa Dawowarta A Tashin Farko Na Samfurin Long March-10B
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    CMG Ya Gabatar Da Shiri Na Musamman Mai Taken “Samun Nasara Dangane Da AI+” A Ketare
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Zargin Da Wasu Sassa Ke Yiwa Kasar Sin Na Takure Sauran Kasashe Masu Tasowa Ba Shi da Tushe Ko Makama
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Ya Raba Buhunan Taki 72,000 Da Kayan Noma Kyauta Ga Manoman Zamfara
  • Sulaiman
    Kasar Sin Ta Fitar Da Shirin Kai Wa Matakin Koli Na Fitar Da Hayakin Carbon
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Nasarar Dawo Da Rokar Da Ake Sarrafa Dawowarta A Tashin Farko Na Samfurin Long March-10B
  • Sulaiman
    CMG Ya Gabatar Da Shiri Na Musamman Mai Taken “Samun Nasara Dangane Da AI+” A Ketare

MASU ALAKA

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka
Ra'ayi Riga

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

July 7, 2026
Next Post
Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

LABARAI MASU NASABA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina

July 11, 2026
Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

July 11, 2026
NAF Ta Kai Hare-Haren Sama Kan Maboyar Ƴan Ta’adda A Borno

NAF Ta Kai Hare-Haren Sama Kan Maboyar Ƴan Ta’adda A Borno

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka

July 11, 2026
Gwamna Dauda Ya Raba Buhunan Taki 72,000 Da Kayan Noma Kyauta Ga Manoman Zamfara

Gwamna Dauda Ya Raba Buhunan Taki 72,000 Da Kayan Noma Kyauta Ga Manoman Zamfara

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello

July 11, 2026
Gwamnati Ta Shirya Gina Gidaje 20,000 Duk Shekara Haɗin Gwuiwar  Jamus

Gwamnati Ta Shirya Gina Gidaje 20,000 Duk Shekara Haɗin Gwuiwar Jamus

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ra’ayin Al’umma Game Da Shirin Gwamnati Na Sake Fasalin Hukumar NYSC

July 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.