Wasu manoma da dama a Arewacin ƙasar nan, musamman ƙananan manoma, har yanzu sun gwammace gudanar da na duƙe tsohon ciniki da galmar shanu.
Hakan ya tilasta su ci gaba da yin noman ne, saboda ci gaba da ƙaruwar tsadar man dizel da ake zuba wa taraktocin noma, musamman duba da cewa; daminar 2026 ta kama.
A cewar manoman, lamarin ya kuma tilasta su, rage yawan noman da suka tsara gudanarwa a kakar noman ta bana, inda suka rugumi yin noman na gargajiya.
Ɗaya daga cikin waɗannan manoman da ya rungumi noman da galmar ta shanu a Ƙaramar Hukumar Lere ta Jihar Kaduna, Alhaji Sani Sulaiman Saminaka ya ce; a kakar ta bana, yin aikin da taraktar noma, ya ragu matuƙa, saɓanin yadda manoman suka yi amfani da ita a noman kakar bara.
Ya ce, kuɗin da aka kashe a gonar da aka yi aiki a bara, ya kai kimanin naira 50,000, amma a bana, saboda tsadar Man Dizel, ya dakatar da noma da dama a yankin.
“A 2025, litar man dizel ɗaya, ya kai kimanin naira 1,000, amma a 2026, lita ɗaya ya haura sama da naira 2,000, wanda a bara, na kashe sama da naira miliyan ɗaya, wajen yin hayar tarkatar noma,” a cewarsa.
Shi ma, Alh. Lawal Abubakar, hayar taraktar ta yi tsada matuƙa, saboda tashin farashin dizel, inda ya ce; gonar da za a iya kashe naira 100,000, domin yin haro, yanzu sai an kashe kimainin naira 150,000, wacce kuma za a iya kashe naira 40,000, yanzu sai an kashe kimanin naira 60,000.
Kazalila, wani manomi Alh. Abdul Shitu ya ce; saboda wannan tashin gwauron zabi ne, ya sanya muka gwammace yin noman da galmar shanu.
Ya ce, yin noman da taraktar, tsadar ta kai naira 300,000, amma hayar galmar shanun, ta kai kimanin naira 150,000.
“Ban taɓa karɓar hayar galmar shanu don yin noma ba, amma a bana, tsadar man dizel, ya tilasata ni yin hakan.
Shitu ya kuma buƙaci matakan gwamnatin tarayya da na jiha da kuma na ƙananan hukumomi, da su samar wa da manoma takin zamani a cikin farashi mai rahusa, domin rage musu wahalhalun noma.














