Masu Masana’antun Kiwon Kajin Gidan Gona a ƙasar nan, sun soki haɗakar gwamnatin ƙasar da ƙasar Chana, ta kimanin dala miliyan 900.
Sun yi gargaɗin cewa, wannan haɗaka, za ta iya durƙusar da fannin kiwon kaji a ƙasar, matuƙar ba a wanzar da ita yadda ya kamata ba.
Sun yi sukar ce, a jihar Legas, a hirarsu daban-daban a ƙarƙashin ƙungiyarsu ta masu kiwon ta ƙasa (PAN).
Sukar tasu na zuwa ne, bayan samun rahoton cewa; gwamnatin ƙasar, na kan ƙoƙarin yin haɗaka da ƙasar Chana ta dala miliyan 900, domin yin aikin kiwon kajin gidan gona a ƙasar nan, wanda hakan zai bayar da damar samar da ƙwan kaji miliyan shida a kowace rana.
Gwamnatin na shirin yin hakan ne, domin cike giɓin da ake da shi a ƙasar na samar da wadataccen abinci.
Sai dai, ƴaƴan ƙungiyar ta PAN, sun jaddada cewa; ya zama wajibi gwamnatin mai makon shiga wannan haɗa, ta mayar da hankali wajen ƙara bunƙasa fannin a ƙasar.
Mataimakin shugaban ƙungiyar na Jihar Legas, Foluso Adams ya ce; matuƙar gwamnatin ta wanzar da wannan haɗaka, za ta yi wa fannin ƙasar illa.
Ya yi kira ga gwamnatin, da ta mayar da hankali wajen haɓaka fannin na ƙasar, musamman domin riƙa samar da ƙwai mai yawa a ƙasar.
Shi ma sakataren yaɗa labarai na ƙungiyar ta PAN na ƙasa, Godwin Egbebe, ya yi gargaɗi kan wannan haɗaka, wanda ya ce; za ta iya haifar da gagarumar koma baya ga fannin a faɗin wannan ƙasa.
“Kamata ya yi gwamnatin ƙasar ta fara yin tunini, kan illar da za ta shafi lafiyar ƴan Nijeriya, kafin ta fara tuninin yin wannan haɗaka,” a cewar Egbebe.
Kazalika, ya sanar da cewa; ya kamata gwamnatin ta yi tunini kan ƙarfin samun kuɗaɗen shigar da ƴan Nijeriya ke samu, wanda wannan haɗakar za ta iya shafar hakan.














