ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dabara Ta Rage Ga Mai Shiga Rijiya

by CGTN Hausa and Sulaiman
5 months ago
Rijiya

Tataburzar siyasar da ake yi game da siyasar yankin gabas ta tsakiya na ci gaba da tona asirin yadda turawan yamma ke ci gaba da cin tuwo da miyar bara. Tun daga rikicin yankin Palasdinu zuwa abubuwan da ke faruwa kwanan nan kan batun Iran, duk da a zahiri suna haifar da koma-baya, amma kuma a badini suna kara mayar da burin yammacin duniyar tamkar mafarkin da ba zai taba zama gaskiya ba saboda kiyayyarsu da take karuwa a zukatan al’ummomin yankin.

Bayan harin Amurka da Isra’ila na shekarar 2025 da gajeren rikicin da ya biyo baya, wasu masana sun lura cewa maimakon hakan ya raunana Iran daga zuci, sai ya kara mata kwarin gwiwar karfafa matsayinta na tsaro tare da kara zurfafa dangantakarta ta diflomasiyya musamman da manyan kasashe masu fada-a-ji a yankin Asiya.

Fankamar yammacin duniya ita ce karfin tattalin arziki da kuma makamai. Amma kuma yaki daga zuciya ake cin nasararsa. Ko an zubar da jini, wutar gaba mai ruruwa a zukatan al’umma ba ta mutuwa, sai dai ta sake rincabe nasarar da aka ci. Ga misalai nan a kasashen da Amurka da kawayenta suka afka musu, kamar Afghanistan, Iraqi da Libiya da kuma sauran kasashen da suka yi musu munakisa.

ADVERTISEMENT

Duk da cewa takunkuman da aka kakabawa Iran sun lalata tattalin arzikinta kuma sun shafi rayuwar talakawan kasar, amma kuma ba su samar da tasirin siyasa da Washington ta yi tsammani ba. A halin yanzu, galibin fushin da al’ummar Iran ke yi bisa yanayin da aka jefa su ciki na kara karkata zuwa ga wadanda suka kakaba takunkuman duk kuwa da zanga-zangar da aka yi kwanan baya, saboda haka, matsin tattalin arzikin yammacin duniya bai ba su asalin muradin abin da suke nema ba.

A wani tsokaci da ya yi ta kafar sada zumunta, wani farfesa daga tsangayar nazarin muhalli ta Jami’ar BUK dake Nijeriya, Malam Aliyu Salisu Barau ya yi nuni da cewa, ya kamata kasashen yammacin duniya su fahimci rashin tasirin dabi’ar tilastawa a wannan zamani, inda ya kafa hujja da cewa, sassauta takunkumi da inganta yanayin jin kai na iya sauya ra’ayoyin al’umma fiye da tayar da husuma. Kazalika, kyakkyawar diflomasiyya da hulda ta tattalin arziki na iya samar da yanayi mafi dacewa na ci gaba da kuma zaman lafiya na dogon lokaci.

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

A halin yanzu dai yanayin daidaiton karfin duniya ya sauya sosai ta fuskar wayewa hatta ma da ci gaban tattalin arziki, misali a shekarar 2000, tattalin arzikin Tarayyar Turai ya ninka na kasar Sin sau da yawa, amma zuwa 2025 sun yi kusan kafada da kafada. Kuma hasashe ya nuna cewa zuwa 2050 tattalin arzikin Sin zai iya ninka na Turai sau biyu. Wannan sauyi, a cewar masu sharhi, alama ce ta sake daidaita tasirin duniya a dogon lokaci, kuma yana kalubalantar tsoffin tsare-tsare na kashin dankali dake jagorantar manufofin yammacin duniya. Don haka batun samun sauyi mai ma’ana babu makawa, yanzu dabara ta rage ga mai shiga rijiya! (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Rijiya
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Rijiya
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
Kasuwar Musayar ‘Yan Kwallo: Kante Ya Kammala Komawa Fenerbahce

Kasuwar Musayar 'Yan Kwallo: Kante Ya Kammala Komawa Fenerbahce

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.