ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dabara Ta Rage Ga Mai Shiga Rijiya

by CGTN Hausa and Sulaiman
5 months ago
Rijiya

Tataburzar siyasar da ake yi game da siyasar yankin gabas ta tsakiya na ci gaba da tona asirin yadda turawan yamma ke ci gaba da cin tuwo da miyar bara. Tun daga rikicin yankin Palasdinu zuwa abubuwan da ke faruwa kwanan nan kan batun Iran, duk da a zahiri suna haifar da koma-baya, amma kuma a badini suna kara mayar da burin yammacin duniyar tamkar mafarkin da ba zai taba zama gaskiya ba saboda kiyayyarsu da take karuwa a zukatan al’ummomin yankin.

Bayan harin Amurka da Isra’ila na shekarar 2025 da gajeren rikicin da ya biyo baya, wasu masana sun lura cewa maimakon hakan ya raunana Iran daga zuci, sai ya kara mata kwarin gwiwar karfafa matsayinta na tsaro tare da kara zurfafa dangantakarta ta diflomasiyya musamman da manyan kasashe masu fada-a-ji a yankin Asiya.

Fankamar yammacin duniya ita ce karfin tattalin arziki da kuma makamai. Amma kuma yaki daga zuciya ake cin nasararsa. Ko an zubar da jini, wutar gaba mai ruruwa a zukatan al’umma ba ta mutuwa, sai dai ta sake rincabe nasarar da aka ci. Ga misalai nan a kasashen da Amurka da kawayenta suka afka musu, kamar Afghanistan, Iraqi da Libiya da kuma sauran kasashen da suka yi musu munakisa.

ADVERTISEMENT

Duk da cewa takunkuman da aka kakabawa Iran sun lalata tattalin arzikinta kuma sun shafi rayuwar talakawan kasar, amma kuma ba su samar da tasirin siyasa da Washington ta yi tsammani ba. A halin yanzu, galibin fushin da al’ummar Iran ke yi bisa yanayin da aka jefa su ciki na kara karkata zuwa ga wadanda suka kakaba takunkuman duk kuwa da zanga-zangar da aka yi kwanan baya, saboda haka, matsin tattalin arzikin yammacin duniya bai ba su asalin muradin abin da suke nema ba.

A wani tsokaci da ya yi ta kafar sada zumunta, wani farfesa daga tsangayar nazarin muhalli ta Jami’ar BUK dake Nijeriya, Malam Aliyu Salisu Barau ya yi nuni da cewa, ya kamata kasashen yammacin duniya su fahimci rashin tasirin dabi’ar tilastawa a wannan zamani, inda ya kafa hujja da cewa, sassauta takunkumi da inganta yanayin jin kai na iya sauya ra’ayoyin al’umma fiye da tayar da husuma. Kazalika, kyakkyawar diflomasiyya da hulda ta tattalin arziki na iya samar da yanayi mafi dacewa na ci gaba da kuma zaman lafiya na dogon lokaci.

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

A halin yanzu dai yanayin daidaiton karfin duniya ya sauya sosai ta fuskar wayewa hatta ma da ci gaban tattalin arziki, misali a shekarar 2000, tattalin arzikin Tarayyar Turai ya ninka na kasar Sin sau da yawa, amma zuwa 2025 sun yi kusan kafada da kafada. Kuma hasashe ya nuna cewa zuwa 2050 tattalin arzikin Sin zai iya ninka na Turai sau biyu. Wannan sauyi, a cewar masu sharhi, alama ce ta sake daidaita tasirin duniya a dogon lokaci, kuma yana kalubalantar tsoffin tsare-tsare na kashin dankali dake jagorantar manufofin yammacin duniya. Don haka batun samun sauyi mai ma’ana babu makawa, yanzu dabara ta rage ga mai shiga rijiya! (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Rijiya
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa
Rijiya
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
  • Sulaiman
    Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba
  • Sulaiman
    Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
  • Sulaiman
    Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

MASU ALAKA

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Next Post
Kasuwar Musayar ‘Yan Kwallo: Kante Ya Kammala Komawa Fenerbahce

Kasuwar Musayar 'Yan Kwallo: Kante Ya Kammala Komawa Fenerbahce

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.