ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalar Amurka, Kaskar Da Ke Shan Jinin Tattalin Arzikin Duniya

by CMG Hausa
4 years ago
Amurka

Domin neman dakile matsalar hauhawar farashin kayayyaki a gida, babban bankin kasar Amurka(FED) ya kara ruwan kudin ajiya da kaso 0.75% a kwanan baya, sau uku a jere ke nan da ya kara ruwan da wannan kaso a shekarar da muke ciki.

Sakamakon matsayin dalar Amurka a tsarin harkokin hada-hadar kudi ta duniya, matakin da FED din ya dauka ya sa darajar dalar Amurka ta karu a kan sauran kudade, baya ga kuma farashin kayayyaki ya karu a duniya, matakin da kuma ya juya matsalar hauhawar farashin kaya da take fuskanta a gida zuwa sauran kasashe da shiyyoyi.

  • Kasashen Tsibiran Pacific Ba Za Su Zamo Makamin Amurka Na Aiwatar Da Siyasar Yanki Ba

An ce, tun bayan karuwar darajar dalar Amurka a wannan shekara, darajar kudade 36 a sauran kasashen duniya ta ragu da a kalla kaso 1/10. Misali a nahiyar Afirka, darajar kudin Rand na kasar Afirka ta Kudu ta ragu da kashi 9.4%, yayin da darajar Pound na kasar Masar ta sauka da kashi 18%. A kasar Ghana ma, ko da yake ta riga ta daga ruwan kudin ajiya zuwa kashi 22% don tinkarar matakin kasar Amurka, duk da haka, darajar kudin kasar na ci gaba da raguwa.

ADVERTISEMENT

A Nijeriya da ta fi karfin tattalin arziki a Afirka, yawan hauhawar farashin kayayyaki ya kai kaso 19.64% a watan Yuli, baya ga kuma adadin ya hau kaso 20.52% a watan Agustan da ya wuce, wanda ya kai wani matsayin kolin tun bayan watan Satumban shekarar 2005.

Abin da kuma ya biyo bayan matsalar hauhawar farashin kayayyaki shi ne dakushewar tattalin arziki, bisa rahoton hasashen tattalin arzikin Afirka na shekarar 2022 da bankin raya Afirka ya fitar a kwanan baya, an yi hasashen bunkasuwar tattalin arzikin Afirka da kaso 4.1% a wannan shekara, wanda ya fado kasa kwatankwacin kaso 6.9% da aka samu a shekarar 2021.

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

Ta hanyar saka matsalar hauhawar farashin kaya ga sauran kasashe, matsalar da Amurka din take fuskanta a cikin gida ta sassauta, duk da cewa hakan ya faru ne sakamakon hasarorin da sauran kasashe suke biya ta fannonin matsalar hauhawar farashin kaya da tabarbarewar tattalin arziki, lallai abin da mai iya magana kan ce, “Amurka ke ciwo, amma ta sa sauran kasashe su sha magani.”

A hakika dai, tun bayan karshen yakin duniya na biyu, Amurka ta sha yin amfani da kakkarfan matsayin dalar Amurka a duniya wajen kwatan arzikin sauran kasashe da ma saka matsalolinta gare su.

Tamkar dai wata kaskar da ke jinin tattalin arzikin duniya ne, yadda Amurka ke amfani da dalarta wajen kwace dukiyoyin al’ummun sauran kasashe.
Hanya mafi kyau wajen daidaita wannan matsala ita ce, a rungumi manufar kiyaye kasancewar bangarori daban daban, wato kamata ya yi kasa da kasa, musamman ma kasashe masu tasowa su tsaya kan aiwatar da hadin gwiwa a tsakaninsu, wajen kafa wani tsarin hada-hadar kudi mai inganci da ke kunshe da kudade na kasashe daban daban. (Mai Zane:Mustapha Bulama)

Amurka
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
2023: Cin Fuska Ne Ga Jonathan A Bukaci Ya Sake Yin Takarar Shugaban Kasa —Bulkachuwa

"Ka Da Ku Kuskura Ku Zaɓi Masu Kashe Mutane A Zaɓen 2023 — Goodluck Jonathan

LABARAI MASU NASABA

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.