A yau Lahadi ne daliban manyan makarantun sakandare na kasar Sin, suka fara rubuta jarabawar neman gurbin shiga manyan makarantun kasar wadda ake kira gaokao, inda ma’aikatar ilimin kasar ta ce adadin daliban da suka yi rajista don rubuta jarabawar a bana suka kai miliyan 12.9.
An dai tsara rubuta jarabawar gaokao ta bana, a yau Lahadi zuwa gobe Litinin, inda wasu yankunan kasar za su gudanar da ita har zuwa ranar Laraba 10 ga watan nan, sakamakon banbancin tsare-tsaren jarabawar wasu darussa.
A duk shekara, ana gudanar da jarabawar ta gaokao ne a watan Yuni, jarabawar da ke zama muhimmiyar kafa ta shiga manyan makarantun kasar Sin, ga miliyoyin daliban manyan makarantun sakandaren kasar.
Gabanin rubuta jarabawar, ma’aikatar ilimin kasar Sin ta yi kira ga hukumomin yankunan kasar da su karfafa tallafinsu ga hidimomin gudanar da ita, ciki har da fannin tsaron al’umma, da sufuri, da ingancin abinci, da kariya daga tsananin zafi, da takaita hayaniya, da kuma hidimomin kwantar da hankulan dalibai masu rubuta jarabawar. (Saminu Alhassan)














Discussion about this post