Gwamnatin Jihar Sakkwato ta bayar da tallafi ga al’ummar ƙauyen Dangulbi da sauran mutanen da harin ‘yan bindiga ya tilasta musu barin gidajensu a Ƙaramar Hukumar Tureta. Tallafin na zuwa ne bayan hare-haren da suka haddasa asarar rayuka da raba mutane da matsugunansu.
Mataimakin Gwamnan Jihar Sakkwato, Alhaji Idris Muhammad Gobir, ne ya kai ziyarar jajantawa ga waɗanda abin ya shafa a ranar Lahadi, inda ya tabbatar musu da cewa gwamnati za ta ɗauki matakan da suka dace domin rage musu raɗaɗin halin da suke ciki. Ya kuma ce gwamnatin jihar na aiki tare da hukumomin tsaro domin dawo da zaman lafiya a yankin.
Gobir ya bayyana cewa gwamnatin ta bayar da tallafin Naira miliyan 30 da buhunan shinkafa 300 ga iyalan waɗanda suka rasa rayukansu sakamakon harin. Ya ƙara da cewa wannan na daga cikin ƙoƙarin gwamnati na tallafa wa waɗanda bala’in ya shafa.
Haka zalika, gwamnatin ta raba buhunan shinkafa 1,200 da Naira miliyan 10 ga ‘yan gudun hijira, sannan ta ware ƙarin Naira miliyan 5 domin kula da waɗanda ke karɓar magani saboda raunukan da suka samu yayin harin.















Discussion about this post