ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Dawowar Kayayyakin Tarihi Gida Shi Ne Ci Gaban Kasashe Masu Tasowa

by Sulaiman and CGTN Hausa
3 months ago
Tarihi

A shekarun nan, a kan ga yadda wata kasa da ta taba yin mulkin mallaka ke mayar da wasu kayayyakin tarihi da ta kwace a baya ga kasashensu na asali.

Kana a kwanan nan, majalisar wakilai ta kasar Faransa ta zartas da wata dokar da za ta saukaka aikin mayar da kayayyakin tarihi da kasar ta kwace daga kasashen da ta taba yi wa mulkin mallaka.

To, duk wadannan ci gaban da aka samu, dalilin su shi ne wani yanayin da ake ciki, na haskakawar tauraron kasashe masu tasowa.Bari mu dauki kasar Faransa a matsayin misali.

ADVERTISEMENT

Da ma kasar ta gabatar da dimbin dokoki don hana mayar da kayan tarihi ga sauran kasashe. Sai dai a wannan karo ta nuna sassauci. Saboda me? Saboda kasar na neman daidaita huldarta da wasu kasashen dake nahiyar Afirka, musamman ma kasashen Mali, da Burkina Faso, da kuma Nijar.

Ta haka muna iya ganin cewa, dawowar kayayyakin tarihi kasashensu na asali ta shafi daga matsayin wadannan kasashen. Ban da haka, ta kuma shafi kokarin da kasashe masu tasowa suke don ganin a mayar musu da kayayyakin tarihi da aka kwace daga hannunsu.

LABARAI MASU NASABA

Binciken Pew: Me Ya Sa Sin Ta Fi Amurka Samun Anincewar Jama’a?

Kada A Bar Kasashe Masu Tasowa A Baya A Zamanin AI

Misali, mun san a Najeriya, an fara neman a dawo da kayayyakin tarihi tun kafuwar kasar a shekarar 1960. Kana a shekarar 2007, an kafa Tawagar Tattaunawa Ta Benin don tattauna batun mayarwa Najeriya da kayayyakin tarihinta masu alaka da al’adun daular Benin. Kana a shekarar 2022, kasar Jamus ta mika ma kasar Najeriya wasu kayayyakin tagulla guda 1130. Kafin daga bisani kasar Holland ta mayarwa Najeriya da kayayyakin tagulla 119 a shekarar 2025.

A nata bangare, kasar Sin ita ma ta yi matukar kokari don neman dawo da kayayyakin tarihinta da aka kwace gida, inda dabarun da ta dauka suka hada da tattauawar jami’ai masu kula da aikin hulda da sauran kasashe, da karfafa hadin gwiwar kasashe daban daban, da dai sauransu.

An ce, tun daga kafuwar jamhuriyar jama’ar kasar Sin a shekarar 1949 har zuwa yanzu kasar ta riga ta dawo da kayayyakin tarihi fiye da dubu 150 cikin gidanta.

Ko da yake aikin neman dawo da kayayyakin tarihi gida yana da wahala sosai, amma su kasashe masu tasowa ba su taba yafe damar yin haka ba. Saboda me? Saboda dole sai an dawo da kayayyakin tarihi masu daraja da ’yan mulkin mallaka suka kwace, sa’an nan za a iya daidaita kura-kuran da aka yi a baya, da tabbatar da adalci a duniya.

Na biyu, shi ne domin kayan tarihi na dauke da tunani mai muhimmanci da ya shafi wata al’umma, don haka ta hanyar dawo da shi za a samu damar karfafa tushen ci gaban harkoki masu alaka da al’adun wata kasa.

Ban da haka, dalili na uku shi ne, yadda hasken kasashen yamma ya dishe ya sa su kasa kiyaye wadannan kayayyakin tarihi yadda ya kamata. Misali a shekarar 2023, cibiyar adana kayayyakin tarihi ta “The British Museum” ta kasar Birtaniya ta sanar da cewa, kayayyakin tarihi kimanin 2000 da ta rike, ciki har da dimbin kayayyakin da aka kwace daga kasashen Afirka, sun bace, ko an sace su, ko kuma sun lalace.

Sa’an nan bisa ra’ayin kasar Sin, yadda ake dawo da kayayyakin tarihi kasashensu na asali zai karfafawa kasashen gwiwa, don su gudanar da nazari da gadon al’adun gargajiya, da samun damar zamanantar da al’umma ta wata hanyar da ta dace da yanayin da suke ciki. (Bello Wang)

Tarihi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Kimi K3 Ya Bayyana Yunkurin Sin Na Raya Fasahar AI A Bayyane Ta Yadda Kowa Zai Amfana
  • Sulaiman
    Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin A Saliyo Ta Fara Horar Da Ma’aikatan Jinya Dabarun Likitancin Gargajiya Na Sin
  • Sulaiman
    Binciken Pew: Me Ya Sa Sin Ta Fi Amurka Samun Anincewar Jama’a?
  • Sulaiman
    Cikakken Jerin Yan Wasan Da Suka Lashe Kyautuka A Gasar Kofin Duniya
Tarihi
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin A Saliyo Ta Fara Horar Da Ma’aikatan Jinya Dabarun Likitancin Gargajiya Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken Pew: Me Ya Sa Sin Ta Fi Amurka Samun Anincewar Jama’a?
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ra’ayin Sin Game Da AI Mai Mayar Da Hankali Kan Bukatun Dan Adam Ya Samu Goyon Bayan Kasa Da Kasa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kada A Bar Kasashe Masu Tasowa A Baya A Zamanin AI

MASU ALAKA

Binciken Pew: Me Ya Sa Sin Ta Fi Amurka Samun Anincewar Jama’a?
Ra'ayi Riga

Binciken Pew: Me Ya Sa Sin Ta Fi Amurka Samun Anincewar Jama’a?

July 20, 2026
Kada A Bar Kasashe Masu Tasowa A Baya A Zamanin AI
Ra'ayi Riga

Kada A Bar Kasashe Masu Tasowa A Baya A Zamanin AI

July 19, 2026
Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI
Ra'ayi Riga

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Next Post
‘Yan Wasa 10 Da Ba Za Su Buga Gasar Kofin Duniya Ba Sakamakon Rauni

'Yan Wasa 10 Da Ba Za Su Buga Gasar Kofin Duniya Ba Sakamakon Rauni

LABARAI MASU NASABA

Shari’ar Malami Ba Za Ta Dakatar Da Burinsa Na Gwamna Ba, Inji Jam’iyyar ADC Ta Kebbi

Shari’ar Malami Ba Za Ta Dakatar Da Burinsa Na Gwamna Ba, Inji Jam’iyyar ADC Ta Kebbi

July 20, 2026
Kimi K3 Ya Bayyana Yunkurin Sin Na Raya Fasahar AI A Bayyane Ta Yadda Kowa Zai Amfana

Kimi K3 Ya Bayyana Yunkurin Sin Na Raya Fasahar AI A Bayyane Ta Yadda Kowa Zai Amfana

July 20, 2026
Kwamandojin Kungiyar Ansaru Biyu Sun Amsa Laifin Garkuwa Da Mutane A Kotu

Kwamandojin Kungiyar Ansaru Biyu Sun Amsa Laifin Garkuwa Da Mutane A Kotu

July 20, 2026
Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin A Saliyo Ta Fara Horar Da Ma’aikatan Jinya Dabarun Likitancin Gargajiya Na Sin

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin A Saliyo Ta Fara Horar Da Ma’aikatan Jinya Dabarun Likitancin Gargajiya Na Sin

July 20, 2026
ICPC Ta Yi Karar Likitan El-Rufai Kan Ƙirƙirar Jabun Rahoton Lafiya

ICPC Ta Yi Karar Likitan El-Rufai Kan Ƙirƙirar Jabun Rahoton Lafiya

July 20, 2026
Binciken Pew: Me Ya Sa Sin Ta Fi Amurka Samun Anincewar Jama’a?

Binciken Pew: Me Ya Sa Sin Ta Fi Amurka Samun Anincewar Jama’a?

July 20, 2026
Cikakken Jerin Yan Wasan Da Suka Lashe Kyautuka A Gasar Kofin Duniya

Cikakken Jerin Yan Wasan Da Suka Lashe Kyautuka A Gasar Kofin Duniya

July 20, 2026
Sojoji Sun Kama Wani Ɗan Sudan Da Ake Zargi Da Haɗa Kai Da ’Yan Ta’adda A Borno

Sojoji Sun Kama Wani Ɗan Sudan Da Ake Zargi Da Haɗa Kai Da ’Yan Ta’adda A Borno

July 20, 2026
Matashi Ya Mutu, Wasu Da Dama Sun Jikkata Yayin Murnar Lashe Kofin Duniya Da Spain Ta Yi

Matashi Ya Mutu, Wasu Da Dama Sun Jikkata Yayin Murnar Lashe Kofin Duniya Da Spain Ta Yi

July 20, 2026
Mbappé Ya Zama Mafi Yawan Ƙwallaye A Tarihin Gasar Kofin Duniya

Mbappé Ya Zama Mafi Yawan Ƙwallaye A Tarihin Gasar Kofin Duniya

July 20, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.