ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Dawowar Kayayyakin Tarihi Gida Shi Ne Ci Gaban Kasashe Masu Tasowa

by Sulaiman and CGTN Hausa
2 months ago
Tarihi

A shekarun nan, a kan ga yadda wata kasa da ta taba yin mulkin mallaka ke mayar da wasu kayayyakin tarihi da ta kwace a baya ga kasashensu na asali.

Kana a kwanan nan, majalisar wakilai ta kasar Faransa ta zartas da wata dokar da za ta saukaka aikin mayar da kayayyakin tarihi da kasar ta kwace daga kasashen da ta taba yi wa mulkin mallaka.

To, duk wadannan ci gaban da aka samu, dalilin su shi ne wani yanayin da ake ciki, na haskakawar tauraron kasashe masu tasowa.Bari mu dauki kasar Faransa a matsayin misali.

ADVERTISEMENT

Da ma kasar ta gabatar da dimbin dokoki don hana mayar da kayan tarihi ga sauran kasashe. Sai dai a wannan karo ta nuna sassauci. Saboda me? Saboda kasar na neman daidaita huldarta da wasu kasashen dake nahiyar Afirka, musamman ma kasashen Mali, da Burkina Faso, da kuma Nijar.

Ta haka muna iya ganin cewa, dawowar kayayyakin tarihi kasashensu na asali ta shafi daga matsayin wadannan kasashen. Ban da haka, ta kuma shafi kokarin da kasashe masu tasowa suke don ganin a mayar musu da kayayyakin tarihi da aka kwace daga hannunsu.

LABARAI MASU NASABA

Labarin Yin Yuzhen: Sin Tana Hadin Gwiwa Da Ketare Don Cika Alkawarin Kiyaye Muhallin Duniya

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

Misali, mun san a Najeriya, an fara neman a dawo da kayayyakin tarihi tun kafuwar kasar a shekarar 1960. Kana a shekarar 2007, an kafa Tawagar Tattaunawa Ta Benin don tattauna batun mayarwa Najeriya da kayayyakin tarihinta masu alaka da al’adun daular Benin. Kana a shekarar 2022, kasar Jamus ta mika ma kasar Najeriya wasu kayayyakin tagulla guda 1130. Kafin daga bisani kasar Holland ta mayarwa Najeriya da kayayyakin tagulla 119 a shekarar 2025.

A nata bangare, kasar Sin ita ma ta yi matukar kokari don neman dawo da kayayyakin tarihinta da aka kwace gida, inda dabarun da ta dauka suka hada da tattauawar jami’ai masu kula da aikin hulda da sauran kasashe, da karfafa hadin gwiwar kasashe daban daban, da dai sauransu.

An ce, tun daga kafuwar jamhuriyar jama’ar kasar Sin a shekarar 1949 har zuwa yanzu kasar ta riga ta dawo da kayayyakin tarihi fiye da dubu 150 cikin gidanta.

Ko da yake aikin neman dawo da kayayyakin tarihi gida yana da wahala sosai, amma su kasashe masu tasowa ba su taba yafe damar yin haka ba. Saboda me? Saboda dole sai an dawo da kayayyakin tarihi masu daraja da ’yan mulkin mallaka suka kwace, sa’an nan za a iya daidaita kura-kuran da aka yi a baya, da tabbatar da adalci a duniya.

Na biyu, shi ne domin kayan tarihi na dauke da tunani mai muhimmanci da ya shafi wata al’umma, don haka ta hanyar dawo da shi za a samu damar karfafa tushen ci gaban harkoki masu alaka da al’adun wata kasa.

Ban da haka, dalili na uku shi ne, yadda hasken kasashen yamma ya dishe ya sa su kasa kiyaye wadannan kayayyakin tarihi yadda ya kamata. Misali a shekarar 2023, cibiyar adana kayayyakin tarihi ta “The British Museum” ta kasar Birtaniya ta sanar da cewa, kayayyakin tarihi kimanin 2000 da ta rike, ciki har da dimbin kayayyakin da aka kwace daga kasashen Afirka, sun bace, ko an sace su, ko kuma sun lalace.

Sa’an nan bisa ra’ayin kasar Sin, yadda ake dawo da kayayyakin tarihi kasashensu na asali zai karfafawa kasashen gwiwa, don su gudanar da nazari da gadon al’adun gargajiya, da samun damar zamanantar da al’umma ta wata hanyar da ta dace da yanayin da suke ciki. (Bello Wang)

Tarihi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana
  • Sulaiman
    Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya
  • Sulaiman
    Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa
  • Sulaiman
    Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno
Tarihi
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin

MASU ALAKA

Labarin Yin Yuzhen: Sin Tana Hadin Gwiwa Da Ketare Don Cika Alkawarin Kiyaye Muhallin Duniya
Ra'ayi Riga

Labarin Yin Yuzhen: Sin Tana Hadin Gwiwa Da Ketare Don Cika Alkawarin Kiyaye Muhallin Duniya

June 5, 2026
Abokin Jibi Shi Ne Aboki
Ra'ayi Riga

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

June 3, 2026
Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka
Ra'ayi Riga

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

June 1, 2026
Next Post
‘Yan Wasa 10 Da Ba Za Su Buga Gasar Kofin Duniya Ba Sakamakon Rauni

'Yan Wasa 10 Da Ba Za Su Buga Gasar Kofin Duniya Ba Sakamakon Rauni

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja

Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja

June 7, 2026
A Ranar Wasa Kawai Ƴan Wasan Iran Zasu Na Shiga Amurka, Bayan Wasa Su Fice

A Ranar Wasa Kawai Ƴan Wasan Iran Zasu Na Shiga Amurka, Bayan Wasa Su Fice

June 7, 2026
An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato

An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato

June 7, 2026
Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana

Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana

June 7, 2026
NDC Za Ta Fitar Da Sunayen Ƴan Takarar Da Suka Tsallake Tantancewa Yau

NDC Za Ta Fitar Da Sunayen Ƴan Takarar Da Suka Tsallake Tantancewa Yau

June 7, 2026
Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya

Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya

June 7, 2026
Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

June 7, 2026
Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

June 7, 2026
Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna

Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna

June 7, 2026
Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Sare Bishiyoyi A Harabar Gidan Talabijin Na Jihar

Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Sare Bishiyoyi A Harabar Gidan Talabijin Na Jihar

June 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.