A shekarun nan, a kan ga yadda wata kasa da ta taba yin mulkin mallaka ke mayar da wasu kayayyakin tarihi da ta kwace a baya ga kasashensu na asali.
Kana a kwanan nan, majalisar wakilai ta kasar Faransa ta zartas da wata dokar da za ta saukaka aikin mayar da kayayyakin tarihi da kasar ta kwace daga kasashen da ta taba yi wa mulkin mallaka.
To, duk wadannan ci gaban da aka samu, dalilin su shi ne wani yanayin da ake ciki, na haskakawar tauraron kasashe masu tasowa.Bari mu dauki kasar Faransa a matsayin misali.
Da ma kasar ta gabatar da dimbin dokoki don hana mayar da kayan tarihi ga sauran kasashe. Sai dai a wannan karo ta nuna sassauci. Saboda me? Saboda kasar na neman daidaita huldarta da wasu kasashen dake nahiyar Afirka, musamman ma kasashen Mali, da Burkina Faso, da kuma Nijar.
Ta haka muna iya ganin cewa, dawowar kayayyakin tarihi kasashensu na asali ta shafi daga matsayin wadannan kasashen. Ban da haka, ta kuma shafi kokarin da kasashe masu tasowa suke don ganin a mayar musu da kayayyakin tarihi da aka kwace daga hannunsu.
Misali, mun san a Najeriya, an fara neman a dawo da kayayyakin tarihi tun kafuwar kasar a shekarar 1960. Kana a shekarar 2007, an kafa Tawagar Tattaunawa Ta Benin don tattauna batun mayarwa Najeriya da kayayyakin tarihinta masu alaka da al’adun daular Benin. Kana a shekarar 2022, kasar Jamus ta mika ma kasar Najeriya wasu kayayyakin tagulla guda 1130. Kafin daga bisani kasar Holland ta mayarwa Najeriya da kayayyakin tagulla 119 a shekarar 2025.
A nata bangare, kasar Sin ita ma ta yi matukar kokari don neman dawo da kayayyakin tarihinta da aka kwace gida, inda dabarun da ta dauka suka hada da tattauawar jami’ai masu kula da aikin hulda da sauran kasashe, da karfafa hadin gwiwar kasashe daban daban, da dai sauransu.
An ce, tun daga kafuwar jamhuriyar jama’ar kasar Sin a shekarar 1949 har zuwa yanzu kasar ta riga ta dawo da kayayyakin tarihi fiye da dubu 150 cikin gidanta.
Ko da yake aikin neman dawo da kayayyakin tarihi gida yana da wahala sosai, amma su kasashe masu tasowa ba su taba yafe damar yin haka ba. Saboda me? Saboda dole sai an dawo da kayayyakin tarihi masu daraja da ’yan mulkin mallaka suka kwace, sa’an nan za a iya daidaita kura-kuran da aka yi a baya, da tabbatar da adalci a duniya.
Na biyu, shi ne domin kayan tarihi na dauke da tunani mai muhimmanci da ya shafi wata al’umma, don haka ta hanyar dawo da shi za a samu damar karfafa tushen ci gaban harkoki masu alaka da al’adun wata kasa.
Ban da haka, dalili na uku shi ne, yadda hasken kasashen yamma ya dishe ya sa su kasa kiyaye wadannan kayayyakin tarihi yadda ya kamata. Misali a shekarar 2023, cibiyar adana kayayyakin tarihi ta “The British Museum” ta kasar Birtaniya ta sanar da cewa, kayayyakin tarihi kimanin 2000 da ta rike, ciki har da dimbin kayayyakin da aka kwace daga kasashen Afirka, sun bace, ko an sace su, ko kuma sun lalace.
Sa’an nan bisa ra’ayin kasar Sin, yadda ake dawo da kayayyakin tarihi kasashensu na asali zai karfafawa kasashen gwiwa, don su gudanar da nazari da gadon al’adun gargajiya, da samun damar zamanantar da al’umma ta wata hanyar da ta dace da yanayin da suke ciki. (Bello Wang)















Discussion about this post