ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Wasa 10 Da Ba Za Su Buga Gasar Kofin Duniya Ba Sakamakon Rauni

by Sulaiman and Rabilu Sanusi Bena
2 months ago
Kofin Duniya

Yayinda babbar gasar kofin Duniya ta bana da za a buga a kasashen Amurka, Mexico da Canada ke karatowa, akwai manyan yan wasan kwallon kafa da kasashensu sun samu nasarar tsallakawa zuwa gasar amma Ba za su samu damar zuwa ba sakamakon raunin da suka samu, da yake dai zuwa yanzu kasashen basu fitar da jerin yan wasan da zasu wakilcesu ba amma dai akwai wadanda ko an fitar da sunayensu Bazasu samu damar zuwa ba:

Samu Aghehowa (Spain)

Dan wasan gaban Fc Porto Samu Aghehowa ya samu rauni a gwuiwarsa a watan Fabrairu, dan wasan mai shekaru 21, yana daga cikin yan wasa masu zafin nama wajen zura kwallaye da ake ganin zai iya taimakawa tawagar kasar Spain a kokarinta na ganin ta lashe gasar Kofin Duniya.

ADVERTISEMENT

Patrick Agyemang (Amurka)

An cire dan wasan gaban na Amurka daga wasan da ya bugawa Derby County bayan raunin da ya samu a wasan, Agyemang na daga cikin yan wasanda ke karawa tawagar Amurka kwarin gwuiwa a wasanninsu na baya, raunin da ya samu ya zama tamkar koma baya ga tawagar Amurka wadda Mauricio Pochettino ke jagoranta.

LABARAI MASU NASABA

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

Valentin Carboni (Argentina)

Dan wasan tsakiya Valentin Carboni, wanda yanzu haka ke zaman aro a kungiyar Racing, ya ji rauni a gwuiwarsa a watan Fabrairu, wanda hakan ya kawo karshen fatansa na shiga tawagar Argentina, dan wasan mai shekaru 21 ya riga ya samu damar buga wasa tareda manyan yan wasan tawagar ciki har da kyaftin din tawagar Lionel Messi.

Cameron Carter-Vickers (Amurka)

Dan wasan baya Cameron Carter-Vickers har yanzu akwai shakku dangane da zuwansa gasar kofin Duniya ta bana, bayan an yi masa tiyata a farkon kakar wasar bana, duk da cewa bai yanke tsammani gaba daya ba, damarsa ta wakiltar Amurka ta ragu sosai.

Hugo Ekitike (Faransa)

Dan wasan gaba na Liverpool Hugo Ekitike ya samu rauni a jijiya a wasan da Liverpool tayi rashin nasara a hannun PSG a gasar Zakarun Turai, raunin da ya samu zai yi sanadiyar da ba zai buga wani mummunan rauni da ya hana shi shiga gasar Faransa.

Juan Foyth (Argentina)

Dan wasanda ya lashe gasar cin kofin Duniya tareda Argentina a shekarar 2022 Juan Foyth ya samu rauni a gwuiwarsa a watan Janairu yayin da yake bugawa Villarreal wasa, dan wasan bayan zai rasa damar sake wakiltar Argentina a matakin gasar cin kofin Duniya.

Luis Ángel Malagón (Mexico)

Mai tsaron ragar kasar Mexico Luis Ángel Malagón yana murmurewa daga raunin da ya samu, idan bai murmure ba zuwa karshen kakar wasa ta bana hakan zai yiwa tawagar kasar Mexico mummunar illa a shirinta na tabuka abin azo a agani yayinda suke shirin karbar bakuncin gasar.

Joaquin Panichelli (Argentina)

An cire Joaquin Panichelli daga wasan da kungiyarsa ta Strasbourg ta samu nasara bayan ya samu rauni a karo na biyu cikin shekaru biyu, wannan koma-baya ya kawo karshen fatansa na shiga cikin tawagar Argentina ta gasar cin kofin Duniya.

Rodrygo (Brazil)

Tauraron Brazil Rodrygo Kuma dan wasan Real Madrid ba zai buga gasar ba yayinda yake kan murmurewa daga raunin da yake fama dashi, rashinsa babban rashi ne ga tawagar kasar Brazil wadda ke fatan cigaba da zama a matsayi na farko a jerin kasashen da suka fi lashe gasar a tarihi.

Mohammed Salisu (Ghana)

Dan wasan baya na Ghana Mohammed Salisu yana fuskantar yiwuwar rashin wakiltar kasarsa ta Ghana yayinda yake fama da jinya bayan raunin da ya samu a kafarsa a watan Janairu, wanda hakan ya sa ba zai buga wa Ghana wasa ba.

Kofin Duniya
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
  • Sulaiman
    Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
  • Sulaiman
    Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya
Kofin Duniya
Rabilu Sanusi Bena
+ posts Bio
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Turkiyya Ta Zama Ƙasa Ta Biyu Da Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Lionel Messi: Mutum Ko Aljan

MASU ALAKA

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya
Wasanni

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

June 22, 2026
Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
Wasanni

Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

June 21, 2026
FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa
Wasanni

FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa

June 21, 2026
Next Post
Darajar Masana’Antar Manhajoji Ta Kasar Sin Na Iya Zarce Yuan Tiriliyan 20

Darajar Masana'Antar Manhajoji Ta Kasar Sin Na Iya Zarce Yuan Tiriliyan 20

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.