ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Wasa 10 Da Ba Za Su Buga Gasar Kofin Duniya Ba Sakamakon Rauni

by Sulaiman and Rabilu Sanusi Bena
1 month ago
Kofin Duniya

Yayinda babbar gasar kofin Duniya ta bana da za a buga a kasashen Amurka, Mexico da Canada ke karatowa, akwai manyan yan wasan kwallon kafa da kasashensu sun samu nasarar tsallakawa zuwa gasar amma Ba za su samu damar zuwa ba sakamakon raunin da suka samu, da yake dai zuwa yanzu kasashen basu fitar da jerin yan wasan da zasu wakilcesu ba amma dai akwai wadanda ko an fitar da sunayensu Bazasu samu damar zuwa ba:

Samu Aghehowa (Spain)

Dan wasan gaban Fc Porto Samu Aghehowa ya samu rauni a gwuiwarsa a watan Fabrairu, dan wasan mai shekaru 21, yana daga cikin yan wasa masu zafin nama wajen zura kwallaye da ake ganin zai iya taimakawa tawagar kasar Spain a kokarinta na ganin ta lashe gasar Kofin Duniya.

ADVERTISEMENT

Patrick Agyemang (Amurka)

An cire dan wasan gaban na Amurka daga wasan da ya bugawa Derby County bayan raunin da ya samu a wasan, Agyemang na daga cikin yan wasanda ke karawa tawagar Amurka kwarin gwuiwa a wasanninsu na baya, raunin da ya samu ya zama tamkar koma baya ga tawagar Amurka wadda Mauricio Pochettino ke jagoranta.

LABARAI MASU NASABA

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

Valentin Carboni (Argentina)

Dan wasan tsakiya Valentin Carboni, wanda yanzu haka ke zaman aro a kungiyar Racing, ya ji rauni a gwuiwarsa a watan Fabrairu, wanda hakan ya kawo karshen fatansa na shiga tawagar Argentina, dan wasan mai shekaru 21 ya riga ya samu damar buga wasa tareda manyan yan wasan tawagar ciki har da kyaftin din tawagar Lionel Messi.

Cameron Carter-Vickers (Amurka)

Dan wasan baya Cameron Carter-Vickers har yanzu akwai shakku dangane da zuwansa gasar kofin Duniya ta bana, bayan an yi masa tiyata a farkon kakar wasar bana, duk da cewa bai yanke tsammani gaba daya ba, damarsa ta wakiltar Amurka ta ragu sosai.

Hugo Ekitike (Faransa)

Dan wasan gaba na Liverpool Hugo Ekitike ya samu rauni a jijiya a wasan da Liverpool tayi rashin nasara a hannun PSG a gasar Zakarun Turai, raunin da ya samu zai yi sanadiyar da ba zai buga wani mummunan rauni da ya hana shi shiga gasar Faransa.

Juan Foyth (Argentina)

Dan wasanda ya lashe gasar cin kofin Duniya tareda Argentina a shekarar 2022 Juan Foyth ya samu rauni a gwuiwarsa a watan Janairu yayin da yake bugawa Villarreal wasa, dan wasan bayan zai rasa damar sake wakiltar Argentina a matakin gasar cin kofin Duniya.

Luis Ángel Malagón (Mexico)

Mai tsaron ragar kasar Mexico Luis Ángel Malagón yana murmurewa daga raunin da ya samu, idan bai murmure ba zuwa karshen kakar wasa ta bana hakan zai yiwa tawagar kasar Mexico mummunar illa a shirinta na tabuka abin azo a agani yayinda suke shirin karbar bakuncin gasar.

Joaquin Panichelli (Argentina)

An cire Joaquin Panichelli daga wasan da kungiyarsa ta Strasbourg ta samu nasara bayan ya samu rauni a karo na biyu cikin shekaru biyu, wannan koma-baya ya kawo karshen fatansa na shiga cikin tawagar Argentina ta gasar cin kofin Duniya.

Rodrygo (Brazil)

Tauraron Brazil Rodrygo Kuma dan wasan Real Madrid ba zai buga gasar ba yayinda yake kan murmurewa daga raunin da yake fama dashi, rashinsa babban rashi ne ga tawagar kasar Brazil wadda ke fatan cigaba da zama a matsayi na farko a jerin kasashen da suka fi lashe gasar a tarihi.

Mohammed Salisu (Ghana)

Dan wasan baya na Ghana Mohammed Salisu yana fuskantar yiwuwar rashin wakiltar kasarsa ta Ghana yayinda yake fama da jinya bayan raunin da ya samu a kafarsa a watan Janairu, wanda hakan ya sa ba zai buga wa Ghana wasa ba.

Kofin Duniya
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • Sulaiman
    ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP
Kofin Duniya
Rabilu Sanusi Bena
+ posts Bio
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Barcelona Ta Kammala Daukar Anthony Gordon Daga Newcastle

MASU ALAKA

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya
Wasanni

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa
Wasanni

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

June 2, 2026
Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta
Adabi

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta

May 31, 2026
Next Post
Darajar Masana’Antar Manhajoji Ta Kasar Sin Na Iya Zarce Yuan Tiriliyan 20

Darajar Masana'Antar Manhajoji Ta Kasar Sin Na Iya Zarce Yuan Tiriliyan 20

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.