An kaddamar da matsayar hada karfi da karfe, wajen samar da ci gaban bai daya, yayin dandalin kafofin watsa labarai na yankin Asiya da Fasifik, wanda aka bude jiya Asabar a birnin Shenzhen na lardin Guangdong dake kudancin kasar Sin. Karkashin wannan matsaya, membobin dandalin kafofin watsa labarai na yankin Asiya da Fasifik, za su hada gwiwa wajen ingiza ci gaba da walwala a yankin.
Dandalin na wannan karo, ya hallara sama da wakilai 400 daga sama da kasashe da yankunan duniya 40, da kuma wasu hukumomin MDD da hukumomin kasa da kasa. Yayin bikin kaddamar da taron, sassa 16 da suka kafa dandalin daga Sin da kasashen ketare, sun yi hadin gwiwar kafa kwamitin tsare-tsare na shirin kawancen kafofin watsa labaran Asiya da Fasifik.
Dandalin na Shenzhen, ya kuma lura cewa, kungiyar raya tattalin arzikin yankin Asiya da Fasifik ko APEC, ta zamo muhimmin tsarin aiki na raya hadin gwiwar tattalin arziki a shiyyar, wanda ke da matsayi na koli, kuma mai hade dukkanin ayyuka, kana mafi tasiri.
Tun kafuwar kungiyar kusan sama da shekaru 30 da suka gabata, APEC ta ingiza ci gaban shiyyar zuwa sahun gaba a fannin bunkasar tattalin arziki, tare da tallafawa wajen mayar da yankin mafi samun sauye-sauye a tsarin tattalin arzikin duniya.
Wakilai mahalarta dandalin sun bayyana cewa, budadden tsari, da kirkire-kirkire, da hadin gwiwa, suna da matukar muhimmanci wajen ingiza ci gaban shiyyar Asiya da Fasifik. Sun kuma bayyana kudurinsu na bude kofa, da kare tsarin cinikayya tsakanin mabambantan sassa, da samar da bayanai, da karin haske kan manufofi da aikace-aikace, irinsu gina yankin cinikayya marar shinge na yankin Asiya da Fasifik, da dunkule shiyyar wuri guda, da daidaita tsarin raya masana’antu da hada-hadar shigar da hajoji sassan shiyyar.
Kazalika, sun amince da ingiza matakan daidata aiwatar da manufofi, da musayar kwarewa, da fayyace cikakkun nasarorin ci gaba da shiyyar ke samu a fannoni daban daban. (Saminu Alhassan)














