Japan ta gyara “ka’idoji uku da suka yi mata tarnakin fitar da kayan tsaro ga ketare”, da fannoni masu yiwa kasar jagoranci a bangaren, inda ta sassauta takunkumin fitar da makamai masu kisa, tare da samar da babban sauyi ga manufofin tsaro.
Wannan matakin ya sabawa matsayin Japan na “mai ra’ayin zaman lafiya” bayan yakin duniya na biyu, kuma ya keta ka’idar “kayyade makaman Japan don kare kanta kadai”.
Matakin na da zummar bunkasa tattalin arzikin cikin gida, da karfafa masana’antar kera makamai, da kuma nuna tasirin siyasa a yankin.Bugu da kari, game da batun fitar da kayayyakin soja da fasahar soji a nan gaba, Japan za ta dora muhimmanci kan kasashen Asiya da yankin tekun Pasifik, tare da kara hada baki da kara raya kawance da wasu kasashe, don kuntatawa, da kuma yi wa Sin barazana, wanda hakan zai kawo cikas ga tsaron yankin.
Ko shakka babu “Sabon ra’ayin fin karfin soja na Japan” yana kara tayar da hankalin sauran sassa. (Amina Xu)















Discussion about this post