Dakarun rundunar ‘Operation ENDURING PEACE’ sun kashe wasu ‘yan bindiga biyu a wani samame na kwanton bauna da suka kai a ƙaramar hukumar Barkin Ladi da ke Jihar Filato.
An gudanar da samamen ne a yammacin ranar Talata, 21 ga Afrilu, 2026, da misalin ƙarfe 7:49 na dare a yankin Marit kusa da Doruwa Babuje, bayan samun sahihan bayanan sirri kan zirga-zirgar wasu da ake zargin masu aikata laifuka ne a yankin.
A cewar sanarwar rundunar sojin, waɗannan ‘yan bindigar sun kasance suna addabar al’ummomin da ke kusa ta hanyar kai hare-hare, fyade, da kuma fashi da makami.
Sojojin suna hango waɗanda ake zargin, sai suka kafa musu kwanton ɓauna, inda aka yi musayar wuta.
An kashe biyu daga cikin ‘yan bindigar yayin artabun, yayin da sauran suka tsere zuwa cikin dazuzzuka.Binciken da aka gudanar a yankin ya kai ga gano wata bindiga ƙirar gida, harsasai biyar masu tsayi da fadin 7.62x39mm, adda, wuka mai kaifi, da kuma wayar hannu.
Tun daga lokacin, sojojin sun ci gaba da kasancewa a ƙauyukan Marit da Lajam domin tabbatar da tsaron mazauna yankin, yayin da ake ci gaba da ƙoƙarin kamo waɗanda suka tsere.















Discussion about this post