• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dole Ne Amurka Ta Yi Watsi Da Matakin Babakere A Fannin Kimiyya Da Fasaha 

by CGTN Hausa and Sulaiman
7 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Dole Ne Amurka Ta Yi Watsi Da Matakin Babakere A Fannin Kimiyya Da Fasaha 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Litinin 2 ga watan nan, gwamnatin Amurka ta sanar da sabon matakin kayyade fitarwa kasar Sin na’urorin latironi, har ma ta kara shigar da kamfanonin Sin kimanin 140 cikin jerin sunaye wadanda ta hana a shigar musu da wadannan kayayyaki daga Amurka. Ban da wannan kuma, ta tsoma baki cikin harkokin cinikayya dake tsakanin Sin da sauran kasashe.

 

Wannan ne karo na 3 da Amurka ta sanar da irin wannan mataki na kayyade fitarwa kasar Sin na’urorin latironi. Amma Amurka ba ta cimma burinta ba ko kadan.

  • Majalisa Ta Dakatar Da Zama Kan Ƙudirin Dokar Haraji
  • Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Shari’a Da Majalisa Su Yi Aiki Tare Kan Dokar Haraji

Cibiyar nazarin tsare-tsaren duniya ta Amurka ta CSIS ta gabatar da alkaluma dake nuna cewa, daga shekarar 2016 zuwa 2023, yawan kudin cinikin na’urorin latironi tsakanin Sin da kasashe kamar su Amurka, da Japan, da Holland da dai sauransu, ya karu a maimakon raguwa.

 

Labarai Masu Nasaba

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

Ban da wannan kuma, CSIC ta ba da alkaluma masu nuna cewa, tun daga shekarar 2017, yawan kudaden da kamfanoni mafi girma 8 a kasar Sin masu kera na’urorin latironi suka kashe ya karu sosai, inda ya zuwa karshen shekarar 2022, saurin karuwar ya kai kashi 40% bisa na 2021, abin da ya bayyana cewa, Sin na gaggauta kirkiro na’urorin latironi don maye gurbin kayayyaki na Amurka.

 

Jaridar New York Times ta kasar Amurka ta ba da labarin cewa, sana’ar samar da na’urorin latironi na matukar bukatar hadin gwiwar kasa da kasa, kuma Sin tana mallakar kamfanoni masu samar da kayayyaki mafi yawa a duniya, inda ita kanta wata babbar kasuwa ce. Hakan ya sa, hadin kai da kasar Sin a wannan bangare ba shakka dole ne ake yi shi, kuma ya kasance wani bangare na tsarin samar da kayayyaki a duniya.

 

Alal hakika dai, duniya na dunkulewa a wannan bangare, amma matakin da Amurka ke dauka ya kawo cikas ga ciniki tsakanin kasa da kasa, kuma ya keta zaman oda da dokar kasuwa, har ma ya haifar da barazana ga tabbacin tsarin samar da kayayyaki a duniya. An yi hasashen cewa, kamfanoni da dama, ciki har da na Amurka a wannan bangare za su yi hasara.

 

Matsa lamba da Amurka take yi ba zai dakile ci gaban fasaha da kimiyyar kasar Sin ba. Bunkasuwa a wannan bangare na bukatar hadin gwiwar kasa da kasa, ya kamata Amurka ta yi watsi da tunanin babakere, ta kuma rungumi hadin gwiwa, don wannan ita ce hanya mafi dacewa da za ta bi. (Mai zane da rubutu: MINA)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Majalisa Ta Dakatar Da Zama Kan Ƙudirin Dokar Haraji

Next Post

Sin Na Fatan Gwamnatin Amurka Mai Zuwa Za Ta Nuna Kamun Ludayi Mai Kyau A Huldarsu

Related

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…
Ra'ayi Riga

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

4 days ago
Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba
Ra'ayi Riga

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

6 days ago
Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
Ra'ayi Riga

Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

2 weeks ago
Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta
Ra'ayi Riga

Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta

2 weeks ago
Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada
Ra'ayi Riga

Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada

2 weeks ago
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi

2 weeks ago
Next Post
Sin Na Fatan Gwamnatin Amurka Mai Zuwa Za Ta Nuna Kamun Ludayi Mai Kyau A Huldarsu

Sin Na Fatan Gwamnatin Amurka Mai Zuwa Za Ta Nuna Kamun Ludayi Mai Kyau A Huldarsu

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.